An rushe wasu cibiyoyin kasuwanci, ciki har da sanannen shagon Pizza da wasu shagunan sayar da kayan hadin wayoyin salula, a yankin Area 11 da ke Garki, a Babban Birnin Tarayya (Abuja), a ranar Talata.
Abuja Metro ta ruwaito cewa rushe-rushen sun biyo bayan zargin cewa wani sabon mai harkar gine-gine ya mallaki fili da wasu gine-gine na kashin kansa.
Aikin rusau cin ya fara ne da misalin karfe 10:00 na safe, inda aka kawo manyan injinan rushe gine-gine domin gudanar da aikin.
Lokacin da wakilan Abuja Metro suka isa wurin da misalin karfe 1:30 na rana, sun samu ana ci gaba da rushe gine-ginen, yayin da ba a tabbatar da ko wane ne mai filin ba.
An ga ma’aikata da masu shaguna cikin gaggawa suna kwashe kujeru, tebura, kayan hadin wayoyi, kayan aiki da sauran kayayyaki masu daraja kafin a rushe gine-ginen.
Wasu daga cikin wadanda abin ya shafa sun shaida wa wakilan jaridar cewa mai filin ya ba su wa’adin watanni shida su fice daga wurin, kuma wa’adin ya kare tun watanni da suka gabata.
A halin da ake ciki, wasu ma’aikatan shagon Pizza, wadanda suka nemi a boye sunayensu, sun bayyana rushewar a matsayin abin takaici, tare da nuna damuwa kan makomar ayyukansu.
Sun ce rusau din ya zo musu ba zato ba tsammani, kuma wasu daga cikinsu na fargabar shiga cikin jerin masu zaman banza da marasa aikin yi a Nijeriya.
Wasu ma’aikatan sun kuma bayyana cewa reshen shagon yana daukar sama da ma’aikata 20 aiki, tare da nuna fatan cewa kamfanin zai mayar da su aiki zuwa wasu rassansa da ke fadin Babban Birnin Tarayya (FCT).
Kokarin jin ta bakin mahukuntan shagon Pizza da sauran kasuwancin da abin ya shafa bai yi nasara ba, domin jami’ansu sun ki yin magana da manema labarai.
Haka kuma, Abuja Metro ta kasa samun amsa daga sabon mai filin, wanda ake zargin shi ne ke gudanar da aikin rushewar.
Mai magana da yawun Sashen Kula da Tsare-tsaren Gine-gine na Babban Birnin Tarayya (FCDCD) ya shaida wa Abuja Metro cewa hukumar ba ita ce ta gudanar da aikin rushewar ba.













