ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

by Rabi'u Ali Indabawa
44 minutes ago
Abuja

An rushe wasu cibiyoyin kasuwanci, ciki har da sanannen shagon Pizza da wasu shagunan sayar da kayan hadin wayoyin salula, a yankin Area 11 da ke Garki, a Babban Birnin Tarayya (Abuja), a ranar Talata.

Abuja Metro ta ruwaito cewa rushe-rushen sun biyo bayan zargin cewa wani sabon mai harkar gine-gine ya mallaki fili da wasu gine-gine na kashin kansa.

Aikin rusau cin ya fara ne da misalin karfe 10:00 na safe, inda aka kawo manyan injinan rushe gine-gine domin gudanar da aikin.

ADVERTISEMENT

Lokacin da wakilan Abuja Metro suka isa wurin da misalin karfe 1:30 na rana, sun samu ana ci gaba da rushe gine-ginen, yayin da ba a tabbatar da ko wane ne mai filin ba.

An ga ma’aikata da masu shaguna cikin gaggawa suna kwashe kujeru, tebura, kayan hadin wayoyi, kayan aiki da sauran kayayyaki masu daraja kafin a rushe gine-ginen.

LABARAI MASU NASABA

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Wasu daga cikin wadanda abin ya shafa sun shaida wa wakilan jaridar cewa mai filin ya ba su wa’adin watanni shida su fice daga wurin, kuma wa’adin ya kare tun watanni da suka gabata.

A halin da ake ciki, wasu ma’aikatan shagon Pizza, wadanda suka nemi a boye sunayensu, sun bayyana rushewar a matsayin abin takaici, tare da nuna damuwa kan makomar ayyukansu.

Sun ce rusau din ya zo musu ba zato ba tsammani, kuma wasu daga cikinsu na fargabar shiga cikin jerin masu zaman banza da marasa aikin yi a Nijeriya.

Wasu ma’aikatan sun kuma bayyana cewa reshen shagon yana daukar sama da ma’aikata 20 aiki, tare da nuna fatan cewa kamfanin zai mayar da su aiki zuwa wasu rassansa da ke fadin Babban Birnin Tarayya (FCT).

Kokarin jin ta bakin mahukuntan shagon Pizza da sauran kasuwancin da abin ya shafa bai yi nasara ba, domin jami’ansu sun ki yin magana da manema labarai.

Haka kuma, Abuja Metro ta kasa samun amsa daga sabon mai filin, wanda ake zargin shi ne ke gudanar da aikin rushewar.

Mai magana da yawun Sashen Kula da Tsare-tsaren Gine-gine na Babban Birnin Tarayya (FCDCD) ya shaida wa Abuja Metro cewa hukumar ba ita ce ta gudanar da aikin rushewar ba.

Abuja
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
Rahotonni

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.