Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran tafiyar Kwankwasiyya na kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce, a shirye yake da ya sasanta da Gwamna Abba Yusuf biyo bayan saɓanin siyasa da ke tsakaninsu, yana mai cewa kaunarsa ga Gwamna Abba har yanzu tana nan.
Dangantakar siyasar ’yan siyasar biyu ta lalace ne bayan Yusuf ya fice daga jam’iyyar NNPP, wadda ya lashe zaben gwamna na 2023 a karkashinta, zuwa jam’iyyar APC mai mulki, matakin da ya jawo suka daga mabiya tafiyar Kwankwasiyya.
Da yake magana a wata hira da aka wallafa a bidiyon BBC Hausa ranar Litinin, Kwankwaso, wanda shi ma ya fice daga NNPP zuwa jam’iyyar NDC, ya ce kofar sulhu har yanzu a bude take.
Ya jaddada cewa Yusuf ne ya zaɓi ficewa daga tafiyarsu ta siyasa, kuma ba zai kore shi ba idan ya yanke shawarar dawowa.
Kwankwaso ya ce, “Har yanzu ina son Abba kuma ban kore shi ba, shi ne ya tafi. Don haka ba Abba kadai ba, duk wanda ya tafi ya dawo, ba zan ki yafewa ba. Ka dubi Ganduje, cikin shekaru da dama da muka yi tare muna aiki, mun sha samun saɓani sannan mu sake sulhu. Haka siyasa take aiki.”














Discussion about this post