ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

by Sulaiman
1 month ago
Aboki

Hausawa su kan ce “Abokin jibi shi ne aboki”, saboda aboki na gaske ba wanda zai rika zuga ka ba ne, maimakon haka, zai iya ba ka taimako a lokacin da ka gamu da matsala.A kwanakin nan, an samu barkewar annobar Ebola a kasar Congo Kinshasa, inda mutane 321 aka tabbatar da kamuwarsu da cutar, kuma daga cikinsu wasu 41 sun mutu. An ce, kwayoyin cutar da suka haddasa annobar wannan karo, kwayoyi ne nau’in BDBV, wadanda har yanzu babu allurar rigakafi ko magani da za su iya dakile su, kana mutuwar mutane masu kamuwa da cutar ya kan kai kaso 25% zuwa kaso 38%. Sai dai ko da yake cutar na da matukar hadari, amma kasar Sin ba tare da wani jinkiri ba ta samar da taimako ga Afirka. A jiya, wasu kwararru masu ilimin likitanci 5 da kasar Sin ta tura sun isa birnin Kinshasa, inda suka fara samar da taimako a fannin hana yaduwar cutar Ebola a kasar Congo Kinshasa.

Mun san halayyar dan Adam ce, yin kokarin nisanta daga wurin da ake fuskantar wata annoba. Amma wadannan kwararru Sinawa cikin sani sun shiga wannan wuri mai fama da annoba. Hakan ya nuna zumuntar da ake samu tsakanin mutanen kasar Sin da na kasashen Afirka, wadda ta ba su ikon yaki da annoba kafada da kafada. A cewar Mista Lin Jian, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, kasar Sin da kasashen Afirka abokai ne na gaske, wadanda suka taba raba fara daya. Kana a kokarin tinkarar annobar Ebola ta wannan karo, kasar Sin za ta samar da tallafi ga kwamitin kungiyar kasashen Afirka ta AU, da ba da taimako ga cibiyar kandagarkin cututtuka ta nahiyar Afirka, a kokarin karfafa gwiwar kasashen Afirka ta fuskar tinkarar annoba.

Hakika kasar Sin da kasashen Afirka tuni sun taba gudanar da hadin kai a kokarin dakile cutar Ebola. Tsakanin shekarar 2014 da ta 2015, an samu yaduwar cutar Ebola a kasashen Saliyo, da Laberiya, da Guinea, inda kasar Sin ta tura kwararru kimanin 1200 zuwa wuraren da aka samu barkewar cutar don samar da taimako. Kana wadannan kwararru Sinawa sun yi jinyar mutane fiye da 900, da gudanar da gwajin jini na mutane fiye da 9000, da horar da jami’an lafiya fiye da dubu 13. Ban da haka, kasar Sin ta kafa cibiyoyin kula da masu fama da cutar Ebola a kasashen Saliyo da Laberiya, da gina dakin gwajin kwayoyin cuta mai matakin tsaron halittu na 3 a Saliyo, da samar da taimako ga kasashe 7 da suke makwabtaka da kasashen da suka samu barkewar annoba, wajen kafa tsarin hana yaduwar cuta, ta yadda kasar Sin ta samar da gudunmowa a yakin da kasashen yammacin Afirka suka yi da cutar Ebola a wancan karo.

ADVERTISEMENT

Sai dai tushen cimma nasarar yakar annoba shi ne amincewa da juna da aka samu tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, bisa hadin gwiwar da suka yi cikin dogon lokaci. Tun daga lokacin da kasar Sin ta tura tawagar likitoci ta farko zuwa kasar Aljeriya a shekarar 1963, zuwa yanzu kasar ta riga ta tura likitocinta kimanin dubu 26 zuwa kasashe 48 dake nahiyar Afirka, inda suka yi wa mutane miliyan 230 jinya. Kana a cikin dimbin shekaru da suka wuce, kasar Sin ta kafa asibotoci, da dakunan gwajin kwayoyin cuta, da sauran kayayyakin kare lafiyar jama’a a kasashen Afirka, gami da horar da jami’ansu na lafiya fiye da dubu 150.

Dalilin da ya sa kasar Sin gudanar da hadin gwiwa da kasashen Afirka a fannin kiwon lafiya cikin dogon lokaci, shi ne manufar kasar ta gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya. A ganin kasar ta Sin, makomar mutane na mabambantan kasashe a hade suke. Muddin dukkan kasashe sun samu ci gaba, kuma dukkan al’ummun duniya sun samu rayuwa mai inganci, sa’an nan za a iya tabbatar da ci gaban al’ummar dan Adam mai dorewa.Batun shigar kwararru masu ilimin likitanci na kasar Sin cikin wurare masu fama da annobar Ebola dake kasar Congon Kinshasa, ya nuna zumunta, da kauna masu zurfi dake tsakanin bangarorin Sin da Afirka, da imaninsu kan hadin gwiwar da suke yi, a kokarin neman samun ci gaba na bai daya. (Bello Wang)

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Aboki
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
  • Sulaiman
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • Sulaiman
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman
  • Sulaiman
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

MASU ALAKA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Next Post
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.