Hausawa su kan ce “Abokin jibi shi ne aboki”, saboda aboki na gaske ba wanda zai rika zuga ka ba ne, maimakon haka, zai iya ba ka taimako a lokacin da ka gamu da matsala.A kwanakin nan, an samu barkewar annobar Ebola a kasar Congo Kinshasa, inda mutane 321 aka tabbatar da kamuwarsu da cutar, kuma daga cikinsu wasu 41 sun mutu. An ce, kwayoyin cutar da suka haddasa annobar wannan karo, kwayoyi ne nau’in BDBV, wadanda har yanzu babu allurar rigakafi ko magani da za su iya dakile su, kana mutuwar mutane masu kamuwa da cutar ya kan kai kaso 25% zuwa kaso 38%. Sai dai ko da yake cutar na da matukar hadari, amma kasar Sin ba tare da wani jinkiri ba ta samar da taimako ga Afirka. A jiya, wasu kwararru masu ilimin likitanci 5 da kasar Sin ta tura sun isa birnin Kinshasa, inda suka fara samar da taimako a fannin hana yaduwar cutar Ebola a kasar Congo Kinshasa.
Mun san halayyar dan Adam ce, yin kokarin nisanta daga wurin da ake fuskantar wata annoba. Amma wadannan kwararru Sinawa cikin sani sun shiga wannan wuri mai fama da annoba. Hakan ya nuna zumuntar da ake samu tsakanin mutanen kasar Sin da na kasashen Afirka, wadda ta ba su ikon yaki da annoba kafada da kafada. A cewar Mista Lin Jian, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, kasar Sin da kasashen Afirka abokai ne na gaske, wadanda suka taba raba fara daya. Kana a kokarin tinkarar annobar Ebola ta wannan karo, kasar Sin za ta samar da tallafi ga kwamitin kungiyar kasashen Afirka ta AU, da ba da taimako ga cibiyar kandagarkin cututtuka ta nahiyar Afirka, a kokarin karfafa gwiwar kasashen Afirka ta fuskar tinkarar annoba.
Hakika kasar Sin da kasashen Afirka tuni sun taba gudanar da hadin kai a kokarin dakile cutar Ebola. Tsakanin shekarar 2014 da ta 2015, an samu yaduwar cutar Ebola a kasashen Saliyo, da Laberiya, da Guinea, inda kasar Sin ta tura kwararru kimanin 1200 zuwa wuraren da aka samu barkewar cutar don samar da taimako. Kana wadannan kwararru Sinawa sun yi jinyar mutane fiye da 900, da gudanar da gwajin jini na mutane fiye da 9000, da horar da jami’an lafiya fiye da dubu 13. Ban da haka, kasar Sin ta kafa cibiyoyin kula da masu fama da cutar Ebola a kasashen Saliyo da Laberiya, da gina dakin gwajin kwayoyin cuta mai matakin tsaron halittu na 3 a Saliyo, da samar da taimako ga kasashe 7 da suke makwabtaka da kasashen da suka samu barkewar annoba, wajen kafa tsarin hana yaduwar cuta, ta yadda kasar Sin ta samar da gudunmowa a yakin da kasashen yammacin Afirka suka yi da cutar Ebola a wancan karo.
Sai dai tushen cimma nasarar yakar annoba shi ne amincewa da juna da aka samu tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, bisa hadin gwiwar da suka yi cikin dogon lokaci. Tun daga lokacin da kasar Sin ta tura tawagar likitoci ta farko zuwa kasar Aljeriya a shekarar 1963, zuwa yanzu kasar ta riga ta tura likitocinta kimanin dubu 26 zuwa kasashe 48 dake nahiyar Afirka, inda suka yi wa mutane miliyan 230 jinya. Kana a cikin dimbin shekaru da suka wuce, kasar Sin ta kafa asibotoci, da dakunan gwajin kwayoyin cuta, da sauran kayayyakin kare lafiyar jama’a a kasashen Afirka, gami da horar da jami’ansu na lafiya fiye da dubu 150.
Dalilin da ya sa kasar Sin gudanar da hadin gwiwa da kasashen Afirka a fannin kiwon lafiya cikin dogon lokaci, shi ne manufar kasar ta gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya. A ganin kasar ta Sin, makomar mutane na mabambantan kasashe a hade suke. Muddin dukkan kasashe sun samu ci gaba, kuma dukkan al’ummun duniya sun samu rayuwa mai inganci, sa’an nan za a iya tabbatar da ci gaban al’ummar dan Adam mai dorewa.Batun shigar kwararru masu ilimin likitanci na kasar Sin cikin wurare masu fama da annobar Ebola dake kasar Congon Kinshasa, ya nuna zumunta, da kauna masu zurfi dake tsakanin bangarorin Sin da Afirka, da imaninsu kan hadin gwiwar da suke yi, a kokarin neman samun ci gaba na bai daya. (Bello Wang)















Discussion about this post