ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

by Sulaiman
8 hours ago
Mata

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana shirinta na tallafa wa mata, ’yan mata, masu nakasa da sauran marasa galihu sama da miliyan daya a faɗin jihar, a wani mataki da ta ce zai ƙarfafa rayuwar al’umma tare da bunƙasa tattalin arziki.

An bayyana hakan ne a yayin wani taron kwana uku da aka gudanar a Sakkwato kan yadda za a aiwatar da Manufofin Ƙarfafa Tattalin Arzikin Mata na Ƙasa, wato Women’s Economic Empowerment Policy, a Jihar Zamfara cikin shekaru biyar masu zuwa.

Da take jawabi a wajen taron, Kwamishiniyar Harkokin Mata da Ci Gaban Al’umma ta Jihar Zamfara, Dakta Aisha M.Z. Anka, ta ce shirin ya nuna ƙudurin gwamnatin jihar na tabbatar da cewa mata da sauran rukunin jama’a masu rauni sun samu damar inganta rayuwarsu.

ADVERTISEMENT

Dakta Anka, wadda Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci Gaban Al’umma, Alhaji Garba Aliyu Gayari, ya wakilta, ta bayyana cewa bunƙasa ilimin mata, kare haƙƙoƙinsu da kuma tabbatar da shigarsu cikin harkokin kuɗi zai taimaka wajen ƙarfafa iyalai da kuma samar da ci gaba mai ɗorewa a al’umma.

Ta ce gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta nuna aniyarta ta bunƙasa rayuwar mata ta hanyar manufofi da shirye-shiryen da ke ƙarfafa shigarsu cikin ilimi, noma, kiwon lafiya da shugabanci na siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

A cewarta, ba za a iya samun ci gaban tattalin arziki mai ma’ana ba tare da bai wa mata da ’yan mata damar cin gajiyar shirye-shiryen ci gaba ba.“Muna buƙatar ƙarin haɗin gwiwa daga Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya (World Bank) da sauran abokan hulɗar ci gaba domin tallafa wa matan Zamfara ta fuskar zamantakewa, siyasa da tattalin arziki domin samun ci gaba mai ɗorewa,” in ji ta.

Ta kuma buƙaci mahalarta taron da suka haɗa da wakilan hukumomin gwamnati, cibiyoyin gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, sarakunan gargajiya da shugabannin addini da su bayar da gudunmawa mai amfani wajen daidaita manufofin da yanayin rayuwa, al’adu da dabi’un al’ummar Zamfara.Tun da farko, wata ƙwararriyar mai ba da shawara da Shirin Kare Muhalli na Mata (WEP) ya ɗauka aiki, Misis Damaris Uja, ta ce an shirya taron ne domin ƙarfafa mata da matasa wajen samun damar amfani da haƙƙoƙinsu ta hanyar shirye-shiryen ci gaban muhalli, zamantakewa, siyasa da tattalin arziki.

Ta bayyana gurɓacewar muhalli, cin zarafin mata da rashin samun damar shiga harkokin kuɗi a matsayin manyan matsalolin da ke addabar mata da ’yan mata a sassa da dama na ƙasar nan.

A nasa jawabin yayin zaman nazari da tantance manufofin, jagorar taron, Farfesa Magdalyne Dura, ta ce aiwatar da manufofin wata alhakin gama-gari ce da ke buƙatar haɗin kan dukkan masu ruwa da tsaki.

Ta ce nasarar wannan tsari za ta dogara ne kan yadda masu ruwa da tsaki suka fahimci yanayin tattalin arziki da zamantakewar jihar tare da bayar da gudunmawa wajen samar da manufofin da za su dace da muradun al’ummar Zamfara.

Farfesa Dura ta kuma yi kira ga mahalarta taron da su tabbatar an tsara manufofin cikin tsarin da ya dace da al’adun gargajiya da kuma koyarwar addinin Musulunci da ake bi a jihar.A ƙarshe, mahalarta taron sun gabatar da shawarwari daban-daban domin samar da cikakkiyar manufa ta ƙarfafa tattalin arzikin mata, wadda za ta magance buƙatun mata, ’yan mata, masu nakasa da sauran marasa galihu a Jihar Zamfara.

Mata
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Alhazan Nijeriya Sun Fara Dawowa Gida Bayan Kammala Aikin Hajjin 2026
Manyan Labarai

Alhazan Nijeriya Sun Fara Dawowa Gida Bayan Kammala Aikin Hajjin 2026

June 3, 2026
Next Post
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.