ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

by Sulaiman
3 weeks ago
Mata

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana shirinta na tallafa wa mata, ’yan mata, masu nakasa da sauran marasa galihu sama da miliyan daya a faɗin jihar, a wani mataki da ta ce zai ƙarfafa rayuwar al’umma tare da bunƙasa tattalin arziki.

An bayyana hakan ne a yayin wani taron kwana uku da aka gudanar a Sakkwato kan yadda za a aiwatar da Manufofin Ƙarfafa Tattalin Arzikin Mata na Ƙasa, wato Women’s Economic Empowerment Policy, a Jihar Zamfara cikin shekaru biyar masu zuwa.

Da take jawabi a wajen taron, Kwamishiniyar Harkokin Mata da Ci Gaban Al’umma ta Jihar Zamfara, Dakta Aisha M.Z. Anka, ta ce shirin ya nuna ƙudurin gwamnatin jihar na tabbatar da cewa mata da sauran rukunin jama’a masu rauni sun samu damar inganta rayuwarsu.

ADVERTISEMENT

Dakta Anka, wadda Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci Gaban Al’umma, Alhaji Garba Aliyu Gayari, ya wakilta, ta bayyana cewa bunƙasa ilimin mata, kare haƙƙoƙinsu da kuma tabbatar da shigarsu cikin harkokin kuɗi zai taimaka wajen ƙarfafa iyalai da kuma samar da ci gaba mai ɗorewa a al’umma.

Ta ce gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta nuna aniyarta ta bunƙasa rayuwar mata ta hanyar manufofi da shirye-shiryen da ke ƙarfafa shigarsu cikin ilimi, noma, kiwon lafiya da shugabanci na siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

A cewarta, ba za a iya samun ci gaban tattalin arziki mai ma’ana ba tare da bai wa mata da ’yan mata damar cin gajiyar shirye-shiryen ci gaba ba.“Muna buƙatar ƙarin haɗin gwiwa daga Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya (World Bank) da sauran abokan hulɗar ci gaba domin tallafa wa matan Zamfara ta fuskar zamantakewa, siyasa da tattalin arziki domin samun ci gaba mai ɗorewa,” in ji ta.

Ta kuma buƙaci mahalarta taron da suka haɗa da wakilan hukumomin gwamnati, cibiyoyin gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, sarakunan gargajiya da shugabannin addini da su bayar da gudunmawa mai amfani wajen daidaita manufofin da yanayin rayuwa, al’adu da dabi’un al’ummar Zamfara.Tun da farko, wata ƙwararriyar mai ba da shawara da Shirin Kare Muhalli na Mata (WEP) ya ɗauka aiki, Misis Damaris Uja, ta ce an shirya taron ne domin ƙarfafa mata da matasa wajen samun damar amfani da haƙƙoƙinsu ta hanyar shirye-shiryen ci gaban muhalli, zamantakewa, siyasa da tattalin arziki.

Ta bayyana gurɓacewar muhalli, cin zarafin mata da rashin samun damar shiga harkokin kuɗi a matsayin manyan matsalolin da ke addabar mata da ’yan mata a sassa da dama na ƙasar nan.

A nasa jawabin yayin zaman nazari da tantance manufofin, jagorar taron, Farfesa Magdalyne Dura, ta ce aiwatar da manufofin wata alhakin gama-gari ce da ke buƙatar haɗin kan dukkan masu ruwa da tsaki.

Ta ce nasarar wannan tsari za ta dogara ne kan yadda masu ruwa da tsaki suka fahimci yanayin tattalin arziki da zamantakewar jihar tare da bayar da gudunmawa wajen samar da manufofin da za su dace da muradun al’ummar Zamfara.

Farfesa Dura ta kuma yi kira ga mahalarta taron da su tabbatar an tsara manufofin cikin tsarin da ya dace da al’adun gargajiya da kuma koyarwar addinin Musulunci da ake bi a jihar.A ƙarshe, mahalarta taron sun gabatar da shawarwari daban-daban domin samar da cikakkiyar manufa ta ƙarfafa tattalin arzikin mata, wadda za ta magance buƙatun mata, ’yan mata, masu nakasa da sauran marasa galihu a Jihar Zamfara.

Mata
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aike Da Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi Zuwa Majalisar Dattawa

June 23, 2026
Next Post
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.