Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta gargaɗi al’umma da su guji biyan kuɗi ga kowa domin a saka su cikin shirin auren gata da gwamnatin jihar ke gudanarwa.
Mataimakin Babban Kwamandan Hukumar Hisbah, Dakta Mujahideen Aminuddeen, ne ya yi wannan gargaɗi a ranar Laraba a Kano, bayan samun rahotannin cewa wasu mutane na karɓar kuɗi daga masu son cin gajiyar shirin da sunan za su taimaka musu wajen yin rajista.
Aminuddeen ya ce gwamnatin jihar ce ta ɗauki nauyin shirin baki ɗaya, inda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da samar da kuɗaɗen kayan aure, kayan ɗaki, jigilar kayan ɗakin zuwa gidajen ma’aurata, da kuma jarin fara sana’a ga waɗanda za su amfana da shirin.
Ya jaddada cewa babu wani jami’in Hukumar Hisbah ko wakilin gwamnati da aka ba izinin karɓar kuɗi daga duk wanda ke son shiga cikin shirin.
Saboda haka, ya buƙaci duk wanda wani ya nemi ya biya kuɗi domin a saka shi cikin shirin da ya kai rahoton lamarin nan take ga Hukumar Hisbah ko jami’an tsaro domin gudanar da bincike tare da ɗaukar matakin da ya dace.














