Shugabannin jam’iyyar ADC a Jihar Kano sun sake tabbatar da Malam Ibrahim Khalil a matsayin halastaccen ɗan takarar gwamna na jam’iyyar a zaɓen shekarar 2027.
Jam’iyyar ta kuma yi watsi da abin da ta bayyana a matsayin yunƙurin wasu mutane daga waje na kawo cikas ga sakamakon zaɓen fidda gwani na gwamna da aka gudanar a jihar.
An bayyana wannan matsaya ne a ranar Asabar a Cibiyar Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano (NUJ), inda manyan jiga-jigan jam’iyyar suka gana da manema labarai tare da zargin wasu shugabannin jam’iyyar na ƙasa da tsoma baki a harkokinta na reshen Kano.
Da yake magana a madadin shugabannin Jam’iyyar (ESILT) da sauran masu ruwa da tsaki, dattijon jam’iyyar, Alhaji Sulaiman Muhammad Mabo, ya ce reshen Kano na ADC yana nan tsayin daka wajen mara wa Ibrahim Khalil baya.
Ya jaddada cewa jam’iyyar a Kano ba za ta amince da duk wani yunƙuri na sauya zaɓin da mambobinta suka yi ba.















Discussion about this post