ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

by Sulaiman
16 seconds ago
Cikin shege

Salam. Malam, wata ce ta yi cikin shege da wani mutum, sai ta nemi wani daban ya rufa mata asiri ya aureta, yanzu haka ya aure ta. Mene ne hukuncin auren?

Wa’alaikumus salam. Zina sabon Allah ce da kuma yaɗa fasadi a bayan ƙasa. Aure kuwa, sunnar Manzon Allah ne da samar da zuriya mai albarka, sannan kuma an kwaɗaitar da mu yin sa.

Amma Mazhabar Malikiyya, suna ganin matar da aka yi zinar da ita, sai ta yi jini wanda ake kira Istibra’i, kafin a ɗaura mata aure, domin a raba maniyyin zinar da na aure. Kuma idan har an ɗaura aure ba ta yin wannan jinin ba, to za a raba wannan auren ko da sun haifi ƴaƴa, domin suna ganin an ɗaura auren ne a cikin idda, kuma Allah ya hana ɗaura aure a cikin idda. Saboda haka, a wurinsu, wannan auren batacce ne kuma rusasshe.                               

ADVERTISEMENT

Amma Mazhabar Abu Hanifa da Imam Shafi`I, suna ganin macen da ta yi zina, an so ta yi istibra’i kafin ta yi aure, amma idan har an ɗaura auren ba ta yi istibra’i ba, auren yana nan daram, ba za a raba su ba. Kuma suka ƙara da cewa, ko da tana da cikin zinar ne aka ɗaura mata aure, to auren yana nan. Sai dai, Imam Abu Hanifa ya ce; mijin da ta aura, ba zai sadu da ita ba, har sai bayan ta haihu, ko da kuwa cikin zinar nasa ne ko na waninsa.                       

Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce, “Duk wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira, to kada ya shayar da ruwansa ga shukar waninsa,” Abu- dawud 1847.

LABARAI MASU NASABA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

Zan Iya Cin Bashin Banki Na Biya Aikin Hajji?

Domin neman ƙarin bayani, duba AL-MUDAWWANNAH aL-KUBRAH 2\173 da Al-mugni na Ibnu-Khudaamah 8/79.

A fahimtata, fatawar Malikiyya ta fi inganci kafin a yi auren, saboda fita daga sabanin malamai abin so ne, sannan kuma za a kaucewa faɗawa haɗari, amma idan an riga an yi auren, to fatawar Hanafiyya abar lura ce, saboda akwai bambanci tsakanin zina da aure, sai dai ya wajaba su nisanci saduwa kafin ta haihu, saboda hadisin da ya gabata.

Allah ne mafi sani.

Cikin shege
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
  • Sulaiman
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Sulaiman
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Sulaiman
    Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

MASU ALAKA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Cikin shege
Fatawa

Zan Iya Cin Bashin Banki Na Biya Aikin Hajji?

May 16, 2026
Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
Addini

Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…

March 20, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

June 21, 2026
Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

June 21, 2026
Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

June 21, 2026
Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

June 21, 2026
FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran

June 21, 2026
‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.