Cibiyar kandagarki da dakile yaduwar cututtuka ta Afrika (Africa CDC), ta yaba da hadin gwiwar da ake yi da Sin a kokarin nahiyar na yaki da cutar Ebola, yayin da adadin wadanda suka kamu da cutar a kasashen Jamhuriyar Demokradiyyar Congo (DRC) da Uganda ya zarce 650.
Yayin wani taron manema labarai ta kafar intanet da yammacin jiya Alhamis, darakta janar na Africa CDC Jean Kaseya ya yi gargadi cewa, gibin da ke akwai wajen gano wadanda suka yi mu’amala da masu cutar a yankunan da annobar ta shafa a DRC, musammam lardin Ituri, na zaman babban kalubale ga aikin dakile yaduwar cutar.
Ya ce ba a gano da dama daga cikinsu ba, kuma ba a bibiyar wadanda aka gano yadda ya kamata.Haka kuma, darakta janar din ya jinjinawa hadin gwiwarsu da Sin wajen dakile annobar, yana mai bayyana goyon bayan da Sin ke ba kasashen Afrika da ma cibiyar Africa CDC.
Ya kara da cewa, “A Afrika muna aiki da dukkan abokan huldarmu, kuma kasar Sin muhimmiyar abokiyar huldar Afrika ce, inda take aiki da kusan dukkan kasashen Afrika.” Ya ce kasashen Afrika na samun taimako daga kasar Sin ta hanyar tallafin kudi, da taimakon kwararru da kuma kayayyakin kula da lafiyar al’umma. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post