A yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Lin Jian, ya soki dabarar siyasa da sakataren tsaron kasar Philippines Gilberto Teodoro Jr. ke amfani da ita, kwana guda bayan Sin ta sanar da kakaba masa takunkumi tare da iyalinsa.
Da yake tsokaci game da takunkuman, Lin Jian ya bayyana yayin taron manema labarai na yau cewa, sun lura cewa Teodoro na ci gaba da jirkita gaskiya da karya yayin da yake maganganu da bata sunan wasu. Ya kara da cewa, kalamai da ayyukan Teodoro ba abin da yake ikirari ba ne na kare mutuncin kasarsa, wata dabara ce ta siyasa domin cimma muradunsa na kashin kai.
Lin Jian ya kara da cewa, wannan halin ganganci da rashin sanin ya kamata na wasu tsiraru irin Teodoro ne ya ta’azzara rikici tsakanin Sin da Philippines da ma lalata dangantakar kasashen biyu, yana cewa a karshe hakan illa zai yi ga muradu da al’ummar Philippines. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post