Wani rahoton hadin gwiwa da aka fitar a baya bayan nan, ya nuna yadda akasarin lardunan kasar Sin suka cimma manyan nasarori a fannin bunkasa rayuwar al’umma, yayin da kasar ta samu matukar karuwar adadin biranen kasar masu matsayin gundumomi, wadanda suka kai babban matsayi, ko kololuwar matsayin ci gaban rayuwar al’umma.
Rahoton na hadin gwiwa, tsakanin shirin samar da ci gaba na MDD ko UNDP, da cibiyar tsara manufofin ci gaba ta jami’ar Tsinghua, da cibiyar nazarin managarcin tsarin tattalin arziki ta jami’ar Tsinghua, na da taken “Sanya ido kan ci gaban bil’adama na Sin: Nazarin tattalin arziki da ci gaban zamantakewa, da kimar muhalli, a yankuna da biranen kasar Sin”.
Rahoton ya bayyana yadda cikin shekaru 10 da suka gabata, ci gaban tattalin arziki da bunkasar ilimi, suka kasance ginshikan ingiza ci gaban rayuwar al’umma a kasar Sin.
A tsokacinsa, shugaban cibiyar nazarin tsara manufofin ci gaba ta jami’ar Tsinghua Yang Yongheng, ya ce rahoton sakamakon baya bayan nan ne, na hadin gwiwa tsakanin jami’ar Tsinghua da shirin UNDP a fannin nazarin ci gaban bil’adama, bayan fitar da rahoton musamman na ci gaban al’umma a kasar Sin na shekarar 2019.
A nata tsokacin kuwa, shugabar kawance bisa manyan tsare-tsare, da tsara manufofi a hukumar UNDP Violante di Canossa, cewa ta yi nazarin ya fayyace abubuwan da sassan kasa da kasa ke tattaunawa, dangane da makomar ci gaba, musamman la’akari da cewa ci gaban bil’adama da muhalli mai dorewa sun dunkule waje guda, ta yadda ba za a iya raba tsakaninsu ba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post