Tawagar ƙwallon ƙafa za ta tafi birnin Warsaw domin buga wasan sada zumunta da takwararta ta Poland a filin wasa na PGE Narodowy.
Kocin ƙungiyar, Eric Chelle, tare da ƴan wasansa za su yi wannan tafiya ne bayan lashe gasar Unity Cup sakamakon doke Jamaica da ci 2-0 a wasan ƙarshe.
An gayyaci Femi Azeez domin maye gurbin Samuel Chukwueze, yayin da Victor Osimhen da Ademola Lookman suka janye daga wasan. Haka kuma Alhassan Yusuf da Samson Tijani ba za su buga wasan ba saboda matsalolin biza.
Bayan wasan da Poland, Super Eagles za ta kara da Portugal a wani wasan sada zumunta ranar 10 ga Yuni, inda tawagar ke fatan ci gaba da kyakkyawan sakamakon da take samu bayan nasarorin da ta samu a wasanninta na baya-bayan nan.















Discussion about this post