Sanata Adams Oshiomhole ya soki burin Peter Obi na tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027, inda ya ce ɗan kasuwa bai dace ya jagoranci Nijeriya ba.
Da yake magana a shirin Beyond the Headlines na gidan talabijin na TVC, Oshiomhole ya ce ‘yan kasuwa sun fi mayar da hankali kan samun riba maimakon tsara ci gaban ƙasa na dogon lokaci.
Ya kuma zargi Obi da fifita shigo da kayayyaki daga ƙasashen waje maimakon ƙarfafa samar da kayayyaki a cikin gida, yana mai cewa hakan na haddasa asarar ayyukan yi a Nijeriya.
Oshiomhole ya yi watsi da alƙawarin Obi na yin wa’adi ɗaya idan aka zaɓe shi shugaban ƙasa, yana cewa ba zai yiwu a sauya Nijeriya cikin shekaru huɗu kacal ba.
Ya kuma ce Obi bai cika duk alƙawuran da ya ɗauka ba lokacin da yake gwamnan Jihar Anambra.
Tsohon gwamnan Jihar Edo ɗin ya kuma zargi Obi da rashin tsayawa a jam’iyya ɗaya, yana cewa ya bar jam’iyyar APGA duk da cewa a baya ya yi alƙawarin ci gaba da kasancewa cikinta.
Oshiomhole ya kare manufofin tattalin arziƙin Shugaba Bola Tinubu, yana cewa gwamnati na ɗaukar matakai masu wahala amma suna inganta makomar ƙasar.
Kalaman nasa na zuwa ne yayin da shirye-shiryen tunkarar zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027 ke ƙara ɗaukar hankali.














