Shugaban Kwamitin Haɗin Gwiwa na Jihar Kano kan Yaƙi da Shan Miyagun Ƙwayoyi da Safarar Haramtattun Ƙwayoyi, Muhuyi Rimin-Gado, ya gargaɗi ‘yan siyasa da su daina matsa masa lamba domin neman a saki waɗanda ake zargi da kasancewa ‘yan daba ko masu aikata laifukan da suka shafi miyagun ƙwayoyi da aka kama yayin ayyukan kwamitin.
Da yake jawabi a ranar Talata yayin wani taron manema labarai a Kano, Rimin-gado ya ce kwamitin zai gudanar da aikinsa ba tare da nuna son kai ko tsoron kowa ba, yana mai jaddada cewa babu wani mutum, komai matsayinsa na siyasa, da zai yi tasiri kan ayyukan kwamitin.
Ya ce, “Kada wani ɗan siyasa ya zo wajena yana neman na saki wani ɗan daba idan muka kama shi. Wannan Kano ce, kuma dukkanmu ‘yan asalin jihar ne. Ba za mu bari wasu tsirarun mutane su lalata makomar jihar ba.
“Mutum ɗaya tilo da zai iya gaya mini in saki wani shi ne Gwamna. Idan har ya yi hakan, hakan na nufin a fakaice yana neman na yi murabus daga muƙamina.”
Kwamitin, wanda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar, ya ƙunshi wakilai daga hukumomin tsaro daban-daban a jihar, kuma an kafa shi ne domin yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi, safarar haramtattun ƙwayoyi da kuma ayyukan ‘yan daba.














