A yau Juma’a ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da firaministan Koriya ta Arewa Pak Thae Song a birnin Beijing. Pak, memba ne kuma a ofishin siyasa na kwamitin kolin Jam’iyyar ‘yan kwadago ta Koriya ta Arewa, kana mataimakin shugaban hukumar zartarwar kasar.
A yayin ganawarsu, shugaba Xi ya ce, kamata ya yi Sin da Koriya ta Arewa su tabbatar sun gina alakoki, kuma har kullum su taimakawa juna wajen karfafa akidunsu na gurguzu, da ingiza kwazonsu na zamanantarwa. (Saminu Alhassan)
ADVERTISEMENT














