Jami’an tsaro sun yi nasarar daƙile wani hari da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai ƙauyen Gangaren Makurdi da ke Ƙaramar Hukumar Bakori a Jihar Katsina. Bayanai sun nuna cewa lamarin ya faru ne a daren ranar Alhamis, bayan mazauna yankin sun kai rahoton motsin waɗanda ake zargin ga hukumomin tsaro.
Masanin harkokin tsaro da aka fi sani da Bakatsine ne ya bayyana hakan a cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X ranar Juma’a. A cewarsa, da zarar an samu kiran gaggawa, dakarun Brigadiya ta 17 tare da haɗin gwiwar jami’an Ƙungiyar bijilanti (Vigilante Group) da CJTF suka garzaya yankin domin kai ɗauki.
Rahotanni sun ce isowar jami’an tsaron cikin gaggawa ta tilasta wa waɗanda ake zargin tserewa kafin su samu damar kai hari kan al’ummar ƙauyen. Hakan ya taimaka wajen kauce wa abin da ka iya haifar da asarar rayuka ko dukiyoyi.
Bakatsine ya yabawa dakarun soja da jami’an tsaron sa-kai da na CJTF bisa saurin amsa kiran neman agaji da kuma ƙwarewar da suka nuna wajen kare rayuka da al’umma. Sai dai ya ce zuwa lokacin wallafa rahoton, ba a samu rahoton rasa rai, jikkata ko kama wani daga cikin waɗanda ake zargin da kai harin ba.













