Alhazan Nijeriya da suka gudanar da aikin Hajjin 2026 sun fara dawowa gida daga Saudiyya, inda alhazan Jihar Nasarawa suka zama rukunin farko da suka fara dawowa.
Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta ce jirgin MaxAir ne ya ɗauko alhazan Jihar Nasarawa su 560 daga Jiddah zuwa Abuja a ranar Laraba.
Wani kamfanin jirgin sama da ke jigilar alhazai, Flynas, ya sanar da cewa alhazan jihohin Ogun da Kebbi za su fara dawowa ranar 4 ga watan Yuni.
Kamfanin ya ce ya tanadi jirage shida domin tabbatar da dawowar alhazan cikin sauƙi da tsari.
Jiragen Flynas na farko za su ɗauko alhazai daga Jiddah zuwa Abeokuta da Birnin Kebbi, yayin da aka shirya ƙarin jirage a ranar 5 ga watan Yuni.
Jami’an kamfanin sun bayyana cewa Flynas ya yi nasarar jigilar alhazai da jami’ai 11,342 daga Nijeriya zuwa Saudiyya a jirage 30 a lokacin tafiya zuwa aikin Hajji.
Kamfanin zai kuma dawo da alhazan jihohin Kebbi, Legas, Osun, Kaduna, Neja, Ogun da Nasarawa.















Discussion about this post