Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa wasu mutum huɗu hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda samun su da hannu a harin da aka kai Cocin Saint Francis Catholic Church da ke Owo a Jihar Ondo.
Mai shari’a Emeka Nwite ne, ya yanke hukuncin a ranar Laraba, bayan ya tabbatar da cewa waɗanda ake tuhuma sun aikata laifin da ake zarginsu da shi a dukkanin tuhume-tuhume guda tara.
Waɗanda aka yanke wa hukuncin kisa sun haɗa da Idris Abdulmalik Omeiza, Al Qasim Idris, Jamiu Abdulmalik da Abdulhaleem Idris.
Kotu ta umarci a rataye su har sai sun mutu.
Sai dai kotun ta wanke mutum na biyar, Momoh Otuho Abubakar, tare da sallamarsa daga dukkanin tuhume-tuhumen da ake masa.
Harin cocin ya yi sanadin mutuwar aƙalla masu ibada 43, wanda ya zama ɗaya daga cikin munanan hare-haren da aka taɓa kai wa wajen ibada a Nijeriya.















Discussion about this post