ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ta Kwace Kadarorin ‘Yan Nijeriya 8 Masu Alaka Da Boko Haram

by Sulaiman
7 months ago
Amurka

Amurka ta kakaba wa wasu ‘yan Nijeriya 8 takunkumi, kan zargin alaka da kungiyoyin ta’addanci da suka hada da Boko Haram da kungiyar ISIL da kuma laifukan da suka shafi yanar gizo.

Ma’aikatar Baitulmali ta Amurka, ta sanar da sanya takunkumin a cikin wata takarda da ta buga ta ranar 10 ga Fabrairu, ta ofishinta na Kula da kadarorin waje (OFAC).

  • Makomar Nijeriya Na Hannun FIFA – Shehu Dikko
  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 3

Matakin yana kunshe ne a cikin shafuka 3,000 da aka sabunta na “Jerin ‘yan kasa na musamman da aka datse” (Jerin SDN), takardar bayani da ke ba da cikakken bayani ga mutane da kungiyoyin da ke karkashin takunkumin Amurka.

ADVERTISEMENT

A cewar OFAC, suna bai wa mutanen da aka rikewa dukiyoyinsu da abubuwan da suka mallaka a karkashin dokar ta Amurka wa’adi a matsayin wani Bangare na yaki da ta’addanci da sauran takunkumi.

“Wannan littafin na ofishin baitul mali na kula da kaddarorin kasashen waje, an tsara shi ne a matsayin kayan aiki da ke bayar da ainihin sanarwar ayyukan da OFAC ke yi dangane da ‘yan kasa da aka keBe, musamman wadanda aka rike dukiyoyinsu, don taimaka wa jama’a wajen bin aiwatar da takunkumi daban-daban da OFAC ke gudanarwa,” in ji hukumar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Daga cikin wadanda aka bayyana sunayensu, akwai Salih Yusuf Adamu, wanda aka fi sani da Salihu Yusuf, an haife shi a ranar 23 ga watan Agustan 1990. An gano yana da alaka da Boko Haram. Yusuf na daga cikin ‘yan Nijeriya shida da aka yankewa hukunci a shekarar 2022 a Hadaddiyar Daular Larabawa, sakamakon kafa kungiyar Boko Haram, domin tara kudade ga masu tayar da kayar baya a Nijeriya.

An samu kungiyar da laifin yunkurin mika dala 782,000 daga Dubai zuwa Nijeriya.

Babestan Oluwole Ademulero, an haife shi a ranar 4 ga Maris, 1953, an saka shi cikin jerin takunkumin da ya shafi ta’addanci. An gano shi a karkashin wasu da suka hada da Wole A. Babestan da Olatunde Irewole Shofeso.

An kuma nada Abu Abdullah ibn Umar Al-Barnawi, wanda aka fi sani da Ba Idrisa, wanda aka ruwaito an haife shi tsakanin 1989 zuwa 1994 a Maiduguri, Jihar Borno. An sanya shi a karkashin takunkumin da ya shafi ta’addanci.

Abu Musab Al-Barnawi, wanda kuma ake kira da Habib Yusuf, an bayyana shi a matsayin shugaban Boko Haram, kuma an bayyana shekarun haihuwarsadaga tsakanin 1990 zuwa 1995.

Khaled (ko Khalid) Al-Barnawi, an haife shi a shekarar 1976 a Maiduguri, ya fito sau biyu a cikin littafin, kuma an sanya shi cikin jerin wasu da suka hada da Abu Hafsat da Mohammed Usman.

Ibrahim Ali Alhassan, wanda aka haifa a 31 ga watan Janairun 1981, an gano cewa; yana rike da fasfo na Nijeriya, kuma an ce yana zaune ne a Abu Dhabi, Hadaddiyar Daular Larabawa. An kuma alakanta shi da Boko Haram.

Abu Bakr bn Muhammad bn Ali Al-Mainuki, wanda aka fi sani da Abu-Bilal Al-Minuki, wanda aka haifa a 1982 a Mainok, Jihar Borno, an bayyana sunansa ne bisa zargin alaka da kungiyar ISIL.

Nnamdi Orson Benson, an haife shi ranar 21 ga Maris, 1987, an sanya shi cikin jerin wadanda aka sanya wa wannan takunkumi, sakamakon wadanda ake zargi da hannu cikin masu muggan ayyuka da ke amfani da intanet. An kuma gano cewa; yana rike da fasfo na Nijeriya.

Karkashin takunkumin, an rike dukkannin kadarorin mutanen da aka lissafa a cikin ikon Amurka. Sannan kuma, an haramta wa mutanen Amurka baki-daya yin mu’amala da su.

An fitar da takunkumin ne, bisa ga umarnin zartarwa mai lamba 13224, wanda ke auna daidaikun mutane da hukumomin da ke da ruwa da tsaki a ayyukan ta’addanci da kuma bayar da kudaden ta’addanci.

A shekarar 2013 ne, Amurka ta sanya kungiyar Boko Haram a matsayin kungiyar ta’addanci ta kasashen waje.

Amurka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Cutar Mashako

Cutar Lassa: Mutum 44 Sun Kamu, 6 Sun Mutu A Nijeriya Cikin Mako 1

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.