ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ta Kwace Kadarorin ‘Yan Nijeriya 8 Masu Alaka Da Boko Haram

by Sulaiman
5 months ago
Amurka

Amurka ta kakaba wa wasu ‘yan Nijeriya 8 takunkumi, kan zargin alaka da kungiyoyin ta’addanci da suka hada da Boko Haram da kungiyar ISIL da kuma laifukan da suka shafi yanar gizo.

Ma’aikatar Baitulmali ta Amurka, ta sanar da sanya takunkumin a cikin wata takarda da ta buga ta ranar 10 ga Fabrairu, ta ofishinta na Kula da kadarorin waje (OFAC).

  • Makomar Nijeriya Na Hannun FIFA – Shehu Dikko
  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 3

Matakin yana kunshe ne a cikin shafuka 3,000 da aka sabunta na “Jerin ‘yan kasa na musamman da aka datse” (Jerin SDN), takardar bayani da ke ba da cikakken bayani ga mutane da kungiyoyin da ke karkashin takunkumin Amurka.

ADVERTISEMENT

A cewar OFAC, suna bai wa mutanen da aka rikewa dukiyoyinsu da abubuwan da suka mallaka a karkashin dokar ta Amurka wa’adi a matsayin wani Bangare na yaki da ta’addanci da sauran takunkumi.

“Wannan littafin na ofishin baitul mali na kula da kaddarorin kasashen waje, an tsara shi ne a matsayin kayan aiki da ke bayar da ainihin sanarwar ayyukan da OFAC ke yi dangane da ‘yan kasa da aka keBe, musamman wadanda aka rike dukiyoyinsu, don taimaka wa jama’a wajen bin aiwatar da takunkumi daban-daban da OFAC ke gudanarwa,” in ji hukumar.

LABARAI MASU NASABA

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

Daga cikin wadanda aka bayyana sunayensu, akwai Salih Yusuf Adamu, wanda aka fi sani da Salihu Yusuf, an haife shi a ranar 23 ga watan Agustan 1990. An gano yana da alaka da Boko Haram. Yusuf na daga cikin ‘yan Nijeriya shida da aka yankewa hukunci a shekarar 2022 a Hadaddiyar Daular Larabawa, sakamakon kafa kungiyar Boko Haram, domin tara kudade ga masu tayar da kayar baya a Nijeriya.

An samu kungiyar da laifin yunkurin mika dala 782,000 daga Dubai zuwa Nijeriya.

Babestan Oluwole Ademulero, an haife shi a ranar 4 ga Maris, 1953, an saka shi cikin jerin takunkumin da ya shafi ta’addanci. An gano shi a karkashin wasu da suka hada da Wole A. Babestan da Olatunde Irewole Shofeso.

An kuma nada Abu Abdullah ibn Umar Al-Barnawi, wanda aka fi sani da Ba Idrisa, wanda aka ruwaito an haife shi tsakanin 1989 zuwa 1994 a Maiduguri, Jihar Borno. An sanya shi a karkashin takunkumin da ya shafi ta’addanci.

Abu Musab Al-Barnawi, wanda kuma ake kira da Habib Yusuf, an bayyana shi a matsayin shugaban Boko Haram, kuma an bayyana shekarun haihuwarsadaga tsakanin 1990 zuwa 1995.

Khaled (ko Khalid) Al-Barnawi, an haife shi a shekarar 1976 a Maiduguri, ya fito sau biyu a cikin littafin, kuma an sanya shi cikin jerin wasu da suka hada da Abu Hafsat da Mohammed Usman.

Ibrahim Ali Alhassan, wanda aka haifa a 31 ga watan Janairun 1981, an gano cewa; yana rike da fasfo na Nijeriya, kuma an ce yana zaune ne a Abu Dhabi, Hadaddiyar Daular Larabawa. An kuma alakanta shi da Boko Haram.

Abu Bakr bn Muhammad bn Ali Al-Mainuki, wanda aka fi sani da Abu-Bilal Al-Minuki, wanda aka haifa a 1982 a Mainok, Jihar Borno, an bayyana sunansa ne bisa zargin alaka da kungiyar ISIL.

Nnamdi Orson Benson, an haife shi ranar 21 ga Maris, 1987, an sanya shi cikin jerin wadanda aka sanya wa wannan takunkumi, sakamakon wadanda ake zargi da hannu cikin masu muggan ayyuka da ke amfani da intanet. An kuma gano cewa; yana rike da fasfo na Nijeriya.

Karkashin takunkumin, an rike dukkannin kadarorin mutanen da aka lissafa a cikin ikon Amurka. Sannan kuma, an haramta wa mutanen Amurka baki-daya yin mu’amala da su.

An fitar da takunkumin ne, bisa ga umarnin zartarwa mai lamba 13224, wanda ke auna daidaikun mutane da hukumomin da ke da ruwa da tsaki a ayyukan ta’addanci da kuma bayar da kudaden ta’addanci.

A shekarar 2013 ne, Amurka ta sanya kungiyar Boko Haram a matsayin kungiyar ta’addanci ta kasashen waje.

Amurka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina
  • Sulaiman
    Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka
  • Sulaiman
    ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara
  • Sulaiman
    Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

MASU ALAKA

DSS
Manyan Labarai

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Zamfara
Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Next Post
Cutar Mashako

Cutar Lassa: Mutum 44 Sun Kamu, 6 Sun Mutu A Nijeriya Cikin Mako 1

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Amurka

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Amurka

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.