Yau Jumm’a, aka bude taron karawa juna sani na dandalin tattauna batutuwan tsaro na Xiangshan na shekarar 2026 a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.
Kungiyar masana ilmin harkokin soja ta kasar Sin da kungiyar nazarin manyan tsare-tsaren kasashen duniya ta kasar Sin ne suka gudanar da taron cikin hadin gwiwa, bisa taken “Aikin tsaro na duniya: kalubaloli da hanyoyin dake gabanmu”, inda aka gayyaci wakilai da masana sama da guda 120, daga kasashe da kungiyoyin kasa da kasa sama da 40.
A yayin taron, mahalarta sun tattauna game da manyan batutuwan da suka hada da “Tsarin duniya da dokokin duniya”, da “Sabbin kalubalolin tsaro a yankin Asiya da Pacifik”, da “Nauyin kare tsaro a duniya”, da kuma “Yadda za a magance kalubalolin amfani da sabbin fasahohi kan harkokin soja” da dai sauransu.
A bana ake cika shekaru 20 da kafa dandalin tattauna batutuwan tsaro na Xiangshan na Beijing, kuma yayin taron karawa juna sani da ake gudanarwa a wannan karo, za a kira taron musayar ra’ayoyi mai taken “Gudummawar da taron dandalin tattaunawar kasa da kasa ta bayar a fannin kare tsaron duniya”, wato, bikin murnar cika shekaru 20 da kafuwar dandalin tattauna batun tsaro na Xiangshan na Beijing.
A lokacin, za a gayyaci shahararrun wakilan da abin ya shafa, domin waiwayen tarihin dandalin Xiangshan na shekaru 20, da tattauna gudummawar da taron dandalin ya bayar kan fannonin shawarwari cikin yanayi na adalci, da hada kan bangarori daban daban, da warware sabani da dai sauransu. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post