Dakarun rundunar Operation Fansan Yamma (OPFY) na ci gaba da tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda, inda suke aiwatar da jerin hare-haren tsaftace yankuna da aka gano a matsayin mafakarsu.
A wata sanarwa da Aliyu Danja, jami’in yada labarai na Joint Task Force North West ya fitar, ya ce an kaddamar da hare-haren ne da asubahin ranar 4 ga Mayu, 2026, inda suka shafi muhimman wurare ciki har da kauyen Maikwanuga a Karamar Hukumar Talata Mafara, da kuma kauyukan Aljumma, Gidan Dawa, Magami Didi da Tungar Magaji duk a Karamar Hukumar Maradun.
Laftanar Kanal Danja ya kara da cewa yayin farmakin, dakarun sun yi arangama da ‘yan ta’adda a Tungar Magaji, inda suka yi amfani da karfi sosai, suka kashe ‘yan ta’adda biyu tare da tilasta sauran tserewa cikin rudani.
Ya kuma bayyana cewa wannan aiki wani bangare ne na yaki mai dorewa na lalata maboyar ‘yan ta’adda a cikin dajin Bagega zuwa Sunke, domin tabbatar da tsaro mai dorewa ga al’ummomin da abin ya shafa.















Discussion about this post