ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bude Taron Majalisar Wakilan Jama’Ar Kasar Sin A Beijing

by CGTN Hausa
3 years ago
taro

Yau Talata da karfe 9 na safe, aka bude taron majalisar wakilan jama’ar Sin a babban dakin taron jama’ar Sin dake nan birnin Beijing. Wakilai kimani 3000 daga wurare da kabilu da sana’o’i daban-daban ne suke halartar taron, don sauke nauyin dake wuyansu na tsarin mulki da shari’a da dokoki.

A gun taron, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gabatar da rahoton aikin gwamnati a babban zauren taruwar jama’a, inda ya ce gabanin manyan kalubalolin da ake fuskanta a kasashen duniya, da muhimman ayyukan yin kwaskwarima, da neman ci gaba, da tabbatar da zaman karko a cikin gida, JKS a karkashin jagorancin shugaba Xi Jinping, ta hada kai da al’ummomin kabilu daban daban na kasar Sin, wajen warware matsalolin da suka gamu da su, yayin da suke sauke nauyinsu yadda ya kamata, kana sun cimma babbar nasara, da cimma burinsu a fannin raya tattalin arziki da zaman takewar al’umma.

A sa’i daya kuma, an cimma nasarar neman ci gaba mai inganci, da tabbatar da yanayin zaman karko na zamantakewar al’umma, lamarin da ya sa aka sami gagarumin ci gaba a fannin gina zamantakewar al’umma ta zamani bisa tsarin gurguzu a dukkanin fannoni.

ADVERTISEMENT
  • Labaran Karyar Cewa “Tattalin Arzikin Sin Na Dakushewa” Ba sa Tasiri A zukatan Jama’a 

Ya kuma kara da cewa, tattalin arzikin kasar ya bunkasa cikin yanayi mai kyau, inda ma’aunin tattalin arzikin GDPn ya zarce Yuan triliyan 126, adadin da ya karu da kaso 5.2 bisa dari. Kana, an samu ci gaba a fannin gina tsarin masana’antu na zamani, kuma masana’antun gargajiya sun samu kyautatuwa, yayin da sabbin sana’o’i suka bunkasa cikin sauri, kana, wasu manyan sakamakon da aka samu a fannin kirkire-kirkire sun kasance a sahun gaba tsakanin kasashen duniya.

Li Qiang ya kara da cewa, an samu sabbin sakamako a fannonin sabunta kimiyya da fasaha, kana, karfin yin kirkire-kirkire yana karuwa ba tare da tsayawa ba. A sa’i daya kuma, an zurfafa ayyukan yin kwaskwarima a gida da bude kofa ga waje yadda ya kamata, yayin da ake inganta tushen neman bunkasuwa cikin tsaro. Haka zalika kuma, ana kyautata muhallin hallitu cikin yanayin zaman karko, yayin da ake kiyaye zaman al’umma yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Bugu da kari, ya ce, ba abu ne mai sauki ba, samun bunkasuwar tattalin arziki cikin shekarar da ta gabata, bisa kokarin da dukkanin al’ummomin kasar suka yi a fadin kasar, ba kawai an cimma buri a fannin raya tattalin arziki ba kadai, har ma an samu gaggarumin ci gaba a harkoki da dama. Sakamakon da aka samu, ya nuna cewa, a karkashin jagorancin kwamitin tsakiyar JKS da shugaba Xi Jinping, jama’ar kasar Sin ta nuna karfi da basira waje warware kalubalolin dake gabanta. Tabbas ne, kasar Sin za ta sami ci gaba na dindindin, yayin da ake kara samun makoma mai haske.

Majalisar wakilan jama’ar Sin mai wa’adin shekaru 5, hukumar koli ce a bangaren mulkin kasar. Ana gudanar da taron majalisar ne a ko wace shekara, inda ake tattaunawa da kuma yanke shawara kan manyan manufofi da dokoki da nada jami’ai.

Haka kuma, matakin koli ne da jama’ar Sin suke shiga harkokin kasa, lamarin dake bayyana manufar gudanar da siyasa ta dimokuradiyya a cikin tsarin mulki na gurguza mai sigar musamman na kasar Sin. Wannan taron dake gudana, ya kasance taro na biyu na majalisar wakilan jama’ar Sin karo na 14, wanda zai tattauna tare da nazari kan sabon rahoton ayyukan gwamnati, hakan ya sa yake jan hankalin bangarorin daban-daban.

Yayin taron na wannan karo mai wa’adin mako daya, wakilan jama’ar Sin za su saurari rahotannin gwamnatin tare da tattaunawa da gudanar da bincike, da kuma takaita ci gaban da aka samu a bara, da tsai da tafarkin raya kasa a sabuwar shekara.

A sa’i daya kuma, taron zai yi bincike kan rahoton bunkasuwar tattalin arziki da al’ummar kasar, da rahoton kasafin kudi na kwamitin tsakiya da na wuraren daban-daban, har ma da rahoton aiki na kotun koli da na hukumar koli ta bin bahasi ta jama’ar kasar.(Amina Xu\ Maryam Yang)

taro
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
An Sulhunta Gwamnan Kano Da Sheikh Aminu Daurawa

An Sulhunta Gwamnan Kano Da Sheikh Aminu Daurawa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.