Gwamnatin Tarayya ta dakatar da jami’an Hukumar Tsaro na Sibil Difens (NSCDC) 21, ciki har da Kwamandan hukumar na Jihar Neja, Suberu Siyaka Aniviye, tare da kafa kwamiti mai mutum 10 domin binciken mutuwar mutane 37 da ake zargin masu haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, waɗanda suka mutu a hannun hukumar a Minna.
Matakin ya biyo bayan umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na gudanar da cikakken bincike ba tare da katsalandan ba.
Daga cikin jami’an da aka dakatar akwai:
SC Usman Isah Ndamaka
ASCI Hassan Mohammed
CCA Bala Mohammed
CSC Oluwadare Sunday
DCC Obafemi Elvis
CSC Annas Shitto Lamino,
DCC Philip Ajayi
Barr. Stephen Tsado
ASCI Alhassan Mohammed
IC Abdullahi Sale
IC Mohammed Sonfada
CAI Liman Abubakar
CAI Bala Usman
IC Mohammed Jiya
DSC Isah Suleiman
CAI Ahmed Wushishi
IC Sale Adamu
IC Haruna Mohammed
ASCI Aliyu Sallah da
CAI Isah Sanusi, baya ga Kwamanda Aniviye. Ana binciken rawar da jami’an suka taka wajen kamawa, da tsarewa da kuma kula da mutanen da suka mutu.
Kwamiti mai mutum 10 da aka kafa zai samu jagorancin Jonathan Kure, tsohon Mataimakin Darakta-Janar na Hukumar DSS, yayin da Farfesa Isa Hayatu Ciroma, SAN, tsohon Darakta-Janar na Makarantar Koyar da Lauyoyi ta Nijeriya, zai kasance sakataren kwamitin.
Sauran mambobin sun haɗa da AIG Hosea Hassan Karma (mai ritaya), da Farfesa Olayinka Buhari, da wakilin Majalisar Masarautar Minna, da wakilin Gwamnatin Jihar Neja, Alhaji Liman Sulaiman na ƙungiyar masu haƙar ma’adinai ta ƙasa (Miners Association of Nigeria), da Deji Adeyanju, da Zainab Suleiman Okino da Dr George Agbakahi.
An ɗora wa kwamitin alhakin gano sunayen waɗanda suka mutu, da binciken yadda aka kama su da kuma yanayin da aka tsare su, da kuma gano musabbabin mutuwarsu. Haka kuma, kwamitin zai binciki ko akwai sakaci, ko laifi ko wani alhaki daga jami’an da abin ya shafa, tare da bayar da shawarwarin matakin da ya kamata a ɗauka da kuma yiwuwar diyya ga waɗanda abin ya shafa. An ba kwamitin makonni biyu ya kammala bincikensa ya gabatar da rahoto ga Ministan Harkokin Cikin Gida.
Mutuwar mutanen 37 ta faru ne bayan da NSCDC ta kama waɗanda ake zargin masu haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba a yankunan M.I. Wushishi da Lukoto na Jihar Neja a ranakun 15 da 16 ga Satumba, 2026. NSCDC ta ce a farko mutanen sun mutu ne sakamakon zargin ɓarkewar wata cuta, amma bincike da gwaje-gwajen lafiya ne kawai za su tabbatar da ainihin musabbabin mutuwar.














