ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato

by Abubakar Sulaiman
3 hours ago

Ƴan bindiga sun kai hari wata kasuwar kayan lambu a garin Mangu, Ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato, inda suka kashe mutane uku tare da jikkata wasu da dama. Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 8:30 na daren Juma’a, lokacin da ƴan kasuwa da masu sayayya ke shirin rufe kasuwar.

Shugaban Ƙungiyar Ci gaban Mwaghavul (MDA), Bulus Dabit, ya tabbatar da faruwar harin, inda ya ce maharan sun buɗe wuta kan wata mota da ke barin kasuwar. Ya ce harbin ya kashe mata biyu da wani matashi namiji, yayin da ba a kai ga gano sunayen waɗanda aka kashe ba.

Dabit ya ce wasu daga cikin mutanen da ke kusa da wurin sun samu munanan raunuka, ƙarar harbin ya sa mutane suka ruga a guje domin tsira, lamarin da ya janyo ƙarin raunuka. An ce ana tura wasu daga cikin waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos (JUTH) domin kula da su.

ADVERTISEMENT

Wani mutum mai suna John Haruna, wanda shi ma ya tabbatar da harin, ya ce harbin kan mai uwa da wabi ya jefa kasuwar cikin ruɗani, inda mutane suka riƙa gudu ta ɓangarori daban-daban. Dabit ya yi kira ga hukumomin tsaro da su yi amfani da bayanan sirri da fasahar zamani wajen gano waɗanda suka kai harin tare da cafke su.

Harin ya zo ne sa’o’i kaɗan bayan MDA ta bayyana damuwa kan barazanar tsaro da ke ci gaba da fuskantar al’ummomin Mangu, inda ƙungiyar ta yi iƙirarin cewa sama da ƴan ƙabilar Mwaghavul 750 aka kashe a hare-hare tun shekarar 2023. Ƙungiyar ta kuma yi kira da a gudanar da bincike kan kashe-kashen da ake zargin sun faru a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
  • Abubakar Sulaiman
    An Dakatar Da Jami’an NSCDC 21 Kan Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja
  • Abubakar Sulaiman
    Ku Rage Farashin Mai, Ku Sakarwa Ƴan Nijeriya Mara – Atiku Ga Tinubu
  • Abubakar Sulaiman
    Hannun Jarin Matatar Dangote Ya Buɗe Wa Ƴan Nijeriya Ido – FCMB

MASU ALAKA

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu
Manyan Labarai

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

September 19, 2026
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

September 19, 2026
An Dakatar Da Jami’an NSCDC 21 Kan Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja
Labarai

An Dakatar Da Jami’an NSCDC 21 Kan Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja

September 19, 2026
Next Post
2027: Magoyin Bayan Atiku Ya Fice Daga ADC, Ya Goyi Bayan Tinubu

2027: Magoyin Bayan Atiku Ya Fice Daga ADC, Ya Goyi Bayan Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

September 19, 2026
Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Angola: Kasar Sin Tana Da Shugaba Mai Hangen Nesa

Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Angola: Kasar Sin Tana Da Shugaba Mai Hangen Nesa

September 19, 2026
2027: Magoyin Bayan Atiku Ya Fice Daga ADC, Ya Goyi Bayan Tinubu

2027: Magoyin Bayan Atiku Ya Fice Daga ADC, Ya Goyi Bayan Tinubu

September 19, 2026
Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato

Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato

September 19, 2026
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 12, Sun Ceto Mutane 66 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

September 19, 2026
An Dakatar Da Jami’an NSCDC 21 Kan Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja

An Dakatar Da Jami’an NSCDC 21 Kan Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja

September 19, 2026
Ku Rage Farashin Mai, Ku Sakarwa Ƴan Nijeriya Mara – Atiku Ga Tinubu

Ku Rage Farashin Mai, Ku Sakarwa Ƴan Nijeriya Mara – Atiku Ga Tinubu

September 19, 2026
Portugal Ta Gayyaci Ronaldo Gasar UEFA Nations League

Portugal Ta Gayyaci Ronaldo Gasar UEFA Nations League

September 19, 2026
Hannun Jarin Matatar Dangote Ya Buɗe Wa Ƴan Nijeriya Ido – FCMB

Hannun Jarin Matatar Dangote Ya Buɗe Wa Ƴan Nijeriya Ido – FCMB

September 19, 2026
Ku Bar Tinubu Ya Kammala Shekaru 8, Nigeria Forward Ta Nemi Ƴan Siyasar Arewa

Ku Bar Tinubu Ya Kammala Shekaru 8, Nigeria Forward Ta Nemi Ƴan Siyasar Arewa

September 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.