Shugaban Rukunin First City Monument Bank (FCMB), Ladi Balogun, ya ce fara sayar da hannayen jarin Matatar Dangote ga jama’a ya buɗe wa ’yan Nijeriya damar zuba jari a wani babban kamfani mai matakin kasuwanci na duniya, tare da tallata yadda kasuwar hada-hadar hannayen jari ta ƙasa ke ƙara faɗaɗa. Ya bayyana hakan ne a yayin da aka fara karɓar kuɗin masu son sayen hannayen jarin a kasuwar sayar da hannun jari ta Nijeriya da ke Legas.
Matatar Dangote ta fitar da hannun jari biliyan 4.1 a farashin Naira 525 kan kowane hannu, wanda zai iya samar da kusan Naira tiriliyan 2.15 idan an sayar da su baki ɗaya. An buɗe tayin ne ranar 14 ga Satumba 2026, kuma za a rufe shi ranar 13 ga Oktoba 2026. Mafi ƙarancin hannun jarin da mutum zai iya saya shi ne guda 10, wanda ke a farashin Naira 5,250.
Balogun ya ce tayin ya samar da damar da ɗaiɗaikun ƴan Nijeriya za su iya shiga zuba jari a manyan kamfanoni, yayin da masu zuba jari daban-daban, ciki har da ƙananan masu zuba jari, da attajirai, da cibiyoyin zuba jari da masu zuba jari daga ƙasashen waje ke ƙara shiga kasuwar. Ya ce ƙarin hanyoyin sayen hannayen jari ta bankuna, da dillalan hannayen jari da kafafen fintech na taimaka wa jama’a su shiga kasuwar cikin sauƙi.
FCMB Group na da hannu a cikin tayin ta kamfanoninsa guda uku: FCMB Capital Markets a matsayin ɗaya daga cikin masu shirya bayar da hannayen jarin, da CSL Stockbrokers a matsayin dillalin hannayen jarin, sannan First City Monument Bank a matsayin bankin karɓar kuɗi da rarraba hannayen jarin.
Matatar Dangote tana da ikon tace ganga 700,000 na ɗanyen mai a kowace rana, kuma tana da shirin ƙara ƙarfin tace man zuwa kusan ganga miliyan 1.4 a kowace rana. A cewar shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, an tsara tayin ne domin faɗaɗa mallakar matatar, ta yadda ƴan Nijeriya daga sassa da matakan samun kuɗi daban-daban za su samu damar mallakar wani kaso na kamfanin.













