Ɗan takarar jam’iyyar ADC na Majalisar Wakilai a mazaɓar Ezza ta Kudu/Ikwo ta Jihar Ebonyi, Ambasada Ephraim Iyke Nwonu, ya fice daga jam’iyyar tare da komawa jam’iyyar APC mai mulki.
Nwonu, wanda a baya yake goyon bayan ɗan takarar ADC na shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana a Abuja ranar Asabar cewa ya janye daga takarar Majalisar Wakilai domin ya goyi bayan sake zaɓen Shugaba Bola Tinubu.
Duk da cewa har yanzu sunansa yana cikin jerin ‘yan takarar ADC da ke shafin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Nwonu ya ce ya yanke shawarar barin takarar ne saboda goyon bayan Tinubu da kuma gwamnan Jihar Ebonyi.
Ya ce zai haɗa kai da shugabanni da magoya bayan APC a Ebonyi domin ganin Tinubu ya samu nasara a jihar a zaɓen 2027.
Nwonu ya kuma ambaci ayyukan tituna da gadoji da Gwamnatin Tarayya ke yi a Ebonyi da jihohin da ke maƙwabtaka da ita a matsayin wasu daga cikin dalilan da suka sa ya sauya matsayarsa.
Ya ambaci gadar Ndibe Beach da kuma aikin faɗaɗa babbar hanyar Enugu-Abakaliki-Ogoja.
Ya kuma yi iƙirarin cewa gwamnatin Tinubu ta bai wa ‘yan asalin Ebonyi muƙamai 23 a matakin Gwamnatin Tarayya, yana mai cewa hakan ya nuna muhimmiyar kulawa da jihar.
Nwonu ya kuma ce Peter Obi ba zame wa Tinubu barazana a yankin Kudu maso Gabas ba, yana mai cewa Shugaban zai samu gagarumar nasara a yankin.
Ya ce wani binciken da ƙungiyarsa ta gudanar tare da Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Jihar Ebonyi ya nuna cewa da dama daga cikin al’ummar jihar sun fahimci ayyukan gwamnatin Tinubu kuma suna shirin mara masa baya da ƙuri’unsu.














