Rundunar Sojojin Nijeriya ta ce ta kashe ’yan ta’adda 12, ta ceto fiye da mutane 66 da aka yi garkuwa da su, tare da kama sama da mutum 34 da ake zargi da taimaka wa ’yan ta’adda a hare-haren da ta gudanar a sassa daban-daban na ƙasar. Sojojin sun kuma gano tare da lalata bama-bamai 12 da aka binne a kan hanya a Jihar Neja.
Daraktan yaɗa labarai na shalƙwatar kwatar Tsaro, Manjo Janar Michael Onoja, ne ya bayyana hakan ranar Asabar, 19 ga Satumba, 2026. Ya ce ayyukan sun haɗa da kashe ƴan ta’adda, da ceto waɗanda aka sace, da kuma cafke masu samar da kayayyaki da bayar da bayanan sirri ga ƙungiyoyin ta’addanci.
A yankin Arewa ta Tsakiya, sojojin Operation Savannah Shield sun kashe ’yan ta’adda a jihohin Kwara da Neja, tare da kwato makamai da harsasai. A ranar 15 ga Satumba, sun ceto mutum 22 da aka yi garkuwa da su a ƙauyen Muchiya da ke Ƙaramar Hukumar Rafi ta Jihar Neja, bayan da ’yan ta’addan suka tsere suka bar waɗanda suka sace. Haka kuma, an lalata bama-bamai 12 da aka gano a yankunan Neja da Kwara tsakanin 12 da 17 ga Satumba.
A Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas, sojojin sun gudanar da hare-hare a jihohin Kaduna, da Katsina, da Kebbi, da Sakkwato, da Adamawa da Barno, inda suka ceto mutane da dama tare da kama waɗanda ake zargi da taimaka wa masu garkuwa da mutane da ’yan ta’adda. A Barno, sojoji sun ceto mutane 14 a yankunan Armuda da Gava na Ƙaramar Hukumar Gwoza, ciki har da Limamin Ngoshe, Malam Sadiq, wanda aka sace a harin da aka kai garin a ranar 3 ga Maris, 2026.
Haka kuma, sojojin sun gudanar da ayyuka a wasu yankuna, ciki har da jihohin Binuwai, da Taraba, da Edo, da Imo da Delta, inda suka kama waɗanda ake zargi da aikata laifuka, suka kwato makamai da harsasai, tare da tarwatsa wuraren tace ɗanyen mai ba bisa ƙa’ida ba.
Babban Hafsan Tsaron Nijeriya, Janar Olufemi Oluyede, ya yaba wa sojojin da sauran hukumomin tsaro bisa ayyukan, tare da kira ga al’umma da shugabannin gargajiya su ci gaba da ba jami’an tsaro sahihan bayanai domin ƙarfafa tsaro a ƙasar.














