ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, September 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Rage Farashin Mai, Ku Sakarwa Ƴan Nijeriya Mara – Atiku Ga Tinubu

by Abubakar Sulaiman
1 day ago

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya ɗauki matakin gaggawa wajen rage farashin man fetur, yana mai cewa hauhawar farashin makamashi na ƙara tsadar sufuri, da abinci da sauran kayayyaki a Nijeriya.

Atiku ya yi wannan kiran ne ranar Juma’a a Abuja yayin da yake magana kan farashin mai, da tallafin rage raɗaɗin tsadar rayuwa da kuma matsin tattalin arziƙin da ƴan ƙasa ke fuskanta.

Atiku ya ce cire tallafin man fetur tun ranar 29 ga Mayu, 2023 ya jefa iyalai, ma’aikata, da manoma da ƴan kasuwa cikin ƙarin nauyin rayuwa, musamman saboda tashin farashin sufuri da kayan abinci. Ya ce idan farashin makamashi ya tashi, farashin sufuri da samar da kayayyaki ma na tashi, lamarin da a cewarsa ke ƙara rage ƙarfin darajar Naira.

ADVERTISEMENT

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya kuma soki dogaro da tallafin gaggawa wajen rage raɗaɗin tsadar rayuwa, yana mai cewa irin wannan tallafi ba zai maye gurbin manufofin da za su magance tushen matsalar tsadar kayayyaki ba. Ya kuma tunatar da Tinubu cewa a baya ya yi watsi da kiransa na rage farashin mai, inda ya ce shugaban ƙasar ya bayyana shawarar a matsayin wadda ke nuna rashin fahimtar yadda gwamnati da tattalin arziƙi ke aiki.

Atiku ya kuma yi gargaɗi kan shirin gwamnatin tarayya na janye tallafin wutar lantarki daga shekarar 2027, yana mai cewa bai kamata a sake maimaita abin da ya biyo bayan cire tallafin man fetur ba. Ya ce gidaje, da ƙananan ’yan kasuwa da masana’antu sun riga sun fuskanci tsadar wutar lantarki da dizal, don haka cire tallafin ba tare da wasu matakan rage nauyin ba na iya ƙara matsin tattalin arziƙi.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

Atiku ya ce a shirye yake ya bai wa gwamnatin Tinubu tsarin manufofin da zai taimaka wajen rage farashin man fetur, ko da gwamnati za ta aiwatar da shi da wani suna. Ya kuma bayyana wani shirin da ya ce zai aiwatar idan aka zaɓe shi a 2027, wanda zai ƙunshi tallafin samar da man fetur da aka tace a cikin Nijeriya, tare da sa ido da tantancewa.

Ya ce abin da ya fi muhimmanci a gare shi shi ne ƴan Nijeriya su samu sauƙin rayuwa, yana mai cewa “ku bar ’yan Nijeriya su shaƙi iska.”

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro
  • Abubakar Sulaiman
    Tinubu Ya Janye Shirin Halartar UNGA, Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Ƴan Bindiga Suka Kashe Ƴan Kasuwa 3 A Filato

MASU ALAKA

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro
Labarai

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

September 20, 2026
Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha
Labarai

Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

September 20, 2026
An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui
Labarai

An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui

September 20, 2026
Next Post
An Dakatar Da Jami’an NSCDC 21 Kan Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja

An Dakatar Da Jami’an NSCDC 21 Kan Mutuwar Masu Haƙar Ma’adinai A Neja

LABARAI MASU NASABA

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

September 20, 2026
Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su

Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su

September 20, 2026
Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

September 20, 2026
Osimhen Ba Zai Buga Wa Nijeriya Wasannin Madagascar Da Guinea-Bissau Ba

Osimhen Ba Zai Buga Wa Nijeriya Wasannin Madagascar Da Guinea-Bissau Ba

September 20, 2026
An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui

An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui

September 20, 2026
Tinubu Ya Janye Shirin Halartar UNGA, Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya

Tinubu Ya Janye Shirin Halartar UNGA, Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya

September 20, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

September 20, 2026
Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf

Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf

September 20, 2026
NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

September 20, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Shirin Tsaron Abinci Da Tallafawa Matasa A Katsina

September 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.