Ƙungiyar Nigeria Forward Project ta yi kira ga ƴan siyasa da sauran masu ruwa da tsaki a Arewacin Nijeriya da su mutunta tsarin karɓa karɓa, tare da barin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kammala wa’adin shekaru takwas kafin Arewa ta nemi komawa kan kujerar shugaban ƙasa.
An bayyana wannan matsaya ne a ranar Juma’a a Abuja, yayin bikin ƙaddamar da ƙungiyar Nigeria Forward, wadda ta ce an kafa ta ne domin inganta haɗin kan ƙasa, da ƙarfafa shigar ’yan ƙasa cikin harkokin mulki da kuma tallafa wa ci gaba da manufofin gwamnati gabanin zaɓen 2027 da bayan sa.
Ministan Ƙirƙire-Ƙirƙire, da Kimiyya da Fasaha, kuma jagoran yunƙurin, Dr Kingsley Tochukwu Udeh, ya ce manufofin gwamnati na yanzu na neman sauya tattalin arziƙin ƙasar daga gyare-gyare zuwa samar da ababen more rayuwa, sannan zuwa samar da ayyukan yi. Ya ce ƙungiyar za ta taimaka wajen isar da bayanai kan ayyukan gwamnati, da zuba jari da samar da damarmaki ga ƴan ƙasa.
A nasa ɓangaren, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, kuma ɗaya daga cikin jagororin kafa ƙungiyar, Ibrahim Waiya, ya ce bai kamata Arewa ta nemi komawa fadar shugaban ƙasa bayan wa’adi guda na gwamnatin Tinubu ba. Ya ce kammala shekaru takwas zai ba gwamnati damar ci gaba da manufofinta da kuma ƙarfafa abin da ta fara.
Waiya ya kuma ambaci cin gashin kan ƙananan hukumomi, da ƙarin kuɗaɗen da ke zuwa ga ƙananan hukumomi da jihohi, da shirin kafa ƴansandan jihohi a matsayin wasu daga cikin sauye-sauyen da ya ce za su iya inganta mulki da tsaro.
Waiya ya ƙara da cewa ya kamata a daina kallon matsalolin talauci da ci gaban Arewacin Nijeriya a matsayin nauyin shugaban ƙasa kaɗai, yana mai cewa dimokuraɗiyya na buƙatar haɗin gwiwar gwamnati, da ta ƴan ƙasa da sauran masu ruwa da tsaki.














