Babban rukunin gidajen radiyo da talabijin na kasar Sin, wato CMG, da ma’aikatar yayata ayyuka ta jam’iyyar juyin-juya-halin jama’ar Laos, sun gudanar da bikin kaddamar da watsa shirye-shirye masu taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu”, da sauran fina-finai masu bayyana labaran Sin a kasar Laos tun daga jiya Talata a birnin Vientiane.
Babban sakataren jam’iyyar juyin-juya-halin jama’ar Laos, kuma shugaban kasar Thongloun Sisoulith, ya aike da sakon taya murnar kaddamar da nuna shirye-shiryen. A cikin sakon nasa, shugaba Thongloun ya ce shirye-shiryen bayyana labarai, kamar mai taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu”, suna dauke da hikimar falsafar Sin, kuma suna nuna muhimmancin da babban sakatare Xi Jinping ke dorawa ga kare al’adun gargajiya, da hangen nesa a harkokin mulkin kasa da gudanar da harkokin siyasa, da kishin kasa mai zurfi, tare da nuna irin tsananin soyayyar da yake da ita ga tsawon tarihin al’adun Sin, mai tarihin fiye da shekaru dubu 5.
A lokaci guda, fina-finan bayyana labaran sun nuna cewa, al’adun Sinawa su ne tushen kishin kasa, da kuma karfi mai dorewa na bunkasar al’ummarta, wanda ke ciyar da babban burin farfado da al’ummar Sin gaba. Shugaban na Laos ya ce, hakan abin koyi ne mai kyau ga kasarsa, ta fuskar karewa, da kuma yada al’adunta, a matsayin kasa ta musamman yayin da take kokarin samun ci gaban tattalin arziki da zamantakewarta, da kuma ingiza ayyukan gurguzu na Laos. (Amina Xu)















Discussion about this post