Mambobi uku na Majalisar Wakilai ta Tarayya ranar Laraba sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar APC mai mulki zuwa jam’iyyun adawa, lamarin da ke nuna ci gaba da rikice-rikicen cikin gida bayan zabukan fidda gwani na jam’iyyar.
’Yan majalisar sun hada da Hon. Abubakar Baba Zango, mai wakiltar mazaɓar Yola ta Arewa/Yola ta Kudu/Girei ta jihar Adamawa; Hon. Rabilu Bala, mai wakiltar mazaɓar Jama’are/Itas-Gaɗau ta jihar Zamfara; da Hon. Abdullahi El-Rasheed, mai wakiltar mazaɓar Dukku/Nafada ta jihar Gombe.
Yayin da Zango da El-Rasheed suka koma jam’iyyar ADC, Bala kuma ya koma jam’iyyar PRP, inda ya danganta matakin da la’akari da siyasa da kuma abin da ya bayyana a matsayin amincewar al’ummomin mazabunsu bayan sakamakon zabukan fidda gwani na APC.
An karanta takardun sauya shekar ta su ne a zauren majalisar yayin zaman majalisar ta bakin kakakin majalisar, Abbas Tajudeen, wanda ke wakiltar jihar Kaduna a karkashin jam’iyyar APC.















Discussion about this post