A ranar Lahadin makon nan ne aka gudanar da musabaƙar alƙur’ani mai girma karo na 41 a Jos, taron ya gudana ne a babban masallacin Jumma’a na garin Jos a ɗakin taro na JNI, inda aka gudanar da gasar cikin mako guda bayan buɗe taro da addu’a.
A jawabinsa, mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Jos ta arewa, Honorable Kabiru Muhammad Garkuwa, ya ce dole ne a ya dinga taimaka wa wannan musabaƙa, sannan ya yi kira a haɗa kai a Jos da yi wa shugabanni biyayya.A nasa jawabin, babban mai gabatar da lekca, darektan makarantar Albayan, Dakta Nazifi Yunus ya bayyana yadda alƙur’ani ya haɗa kan masu aƙidu daban-daban. Ya kuma bayyana yadda Sahabbai suke yi wa Annabi Muhammad (S A W) biyayya.
Sheik Muhammad Sulaiman ya ce ƙur’ani yana sama da komai. Ya yi kira ga ɗalibai kar su yi gasar don kyaututtuka, su yi don Allah. Sannan ya yi kira a nemi tallafi don gina sakateriya da ofis da kuma ɗakin taro. Shi ma ɗan majalisar dokokin Jihar Filato mai wakiltar Jos ta arewa, Dakkta Adamu Aliyu ya yi godiya don zaɓarsa da aka yi a matsayin mai masaukin baƙi da kuma sanya albarka a taro.
Tshohon ɗan majalisar wakilai, Gwani Muhammad Adam Alkadi, wanda yake tallafa wa musabaƙar tsahon shekaru ya yi jawabin neman ofis da sakateriya, sannan ya yi kira ga ƴaniyasa su yi siyasa ba da gaba ba.
Ya ƙara da cewa sun zauna da Gwamna Caleb Mutfwang, an roƙe su da su janye wa Abubakar Aljumma a kujerar majalisar wakilai kuma sun haƙura.A ƙarshe, an bayar da kyaututtuka ga waɗanda suka yi nasara tun daga izu ɗaya zuwa izu sittin da fassara a matakai daban-daban, a izu 60 da fassara Hanif Kamal ya zo na uku da maki 76.6, Mubarak Abubakar ya zo na biyu da maki 81.8, sai Aminu Alhassan Saeed ya zo na ɗaya da maki 85.4.














