Jiya Alhamis, ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, da shugaban kwamitin kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU, Mahmoud Ali Youssouf, sun yi shawarwari kan manyan tsare-tsare a tsakanin kasar Sin da kungiyar AU karo na 9 a hedkwatar kungiyar AU dake birnin Addis Ababa, fadar mulkin kasar Habasha, tare da halarci bikin kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanyar jama’a a tsakanin Sin da Afirka ta shekarar 2026.
Manyan jami’an biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan inganta zamanantarwar kasashen Sin da Afirka cikin hadin gwiwa, da shawarar inganta jagorancin duniya da Sin ta gabatar, da matakin cire haraji kan kayayyakin da ake shigar da su kasar Sin daga kasashen Afrika, da kafuwar kungiyar shiga tsakani na duniya (IOMed), da kuma ra’ayin neman bunkasuwar yankin kahon Afirka cikin lumana da dai sauransu.
Bangarorin biyu na ganin cewa, ya kamata kasar Sin da kungiyar AU su dukufa wajen kare moriyar kasashe masu tasowa, da nuna goyon baya ga juna domin kare muhimmiyar moriyarsu, da manyan abubuwan dake janyo hankulansu. Haka kuma, sun jaddada cewa, za su zurfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu, domin samar da tasiri mai kyau ga kasa da kasa da shiyya-shiyya bisa kokarinsu na neman zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki.
Haka kuma, Wang Yi da Mahmoud Ali Youssouf sun sake jaddada cewa, za su sa kaimi ga bangarori masu ruwa da tsaki domin aiwatar da yarjejeniyoyin hadin gwiwa da aka kulla tsakanin bangarorin Sin da kungiyar AU yadda ya kamata. Ban da haka, jami’an biyu sun cimma ra’ayi daya kan ci gaba da zurfafa hadin gwiwar dake tsakanin Sin da AU, domin samar da alfanu ga al’ummun bangarorin 2 yadda ake bukata. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post