Kotun Ma’aikata da ke Abuja ta hana Ƙungiyar Likitoci ta Nijeriya (NARD) tsunduma yajin aikin da ta shirya farawa a ranar 12 ga watan Janairu, 2026.
Kotun ta umarci NARD da mambobinta da su dakatar da duk wani yajin aiki, zanga-zanga ko wani mataki da zai iya kawo cikas ga ayyukan lafiya.
- Manyan ‘Yan Siyasar Nijeriya Da Taurarunsu Za Su Haska A 2026
- INEC Ta Fara Kashi Na Biyu Na Rajistar Masu Zabe
Wannan umarni zai ci gaba da aiki har zuwa ranar 21 ga watan Janairu, 2026, lokacin da kotu za ta saurari shari’ar.
ADVERTISEMENT
Gwamnatin Tarayya ce ta shigar da ƙarar a kan NARD da shugabanninta.
A baya, likitocin sun yi barazanar dakatar da ayyukansu saboda gazawar gwamnati wajen aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma da su.















Discussion about this post