An kaddamar da taron masu ruwa da tsaki a fannin kasuwanci na Sin da kasashen Afirka a birnin Addis Ababa fadar mulkin kasar Habasha, inda mahalarta taron suka yi kira da a zurfafa hadin gwiwa tsakanin sassan biyu domin tabbatar da ci gaban bai daya.
Da yake jawabi yayin taron da aka bude a jiya Talata, shugaban hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Afirka AU Mahmoud Ali Youssouf, ya ce kasashen Afirka da Sin sun riga sun kulla dangantaka mai karfi, karkashin dandalin tattauna hadin gwiwa na Sin da Afirka ko FOCAC da sauran shirye-shirye masu nasaba, kuma ya dace kasashen Afirka su yi koyi daga kwarewar samar da ci gaba irin ta Sin.
Kazalika, Youssouf ya jinjinawa manufar kawar da harajin fito ga kasashen Afirka 53 da Sin ta sanar, yana mai kira ga kamfanonin kasar Sin da su kara yawan jarinsu a nahiyar Afirka, ta yadda za a kai ga fadada darajar hajoji, da kara inganta yanayin safararsu tare da kamfanonin Afirka domin samun alfanu na bai daya.
A nasa tsokaci kuwa, shugaban tawagar kasar Sin a kungiyar AU Jiang Feng, cewa ya yi nahiyar Afirka na da makoma mai haske ta fuskar ci gaba, yayin da tsarin sarrafa hajoji, da rarraba su na kasar Sin ke da babban kuzari.
Don haka akwai tarin damammaki masu yawa na hadin gwiwa a bangaren noma, da sarrafa hajojin masana’antu, da sabbin makamashi, da tattalin arziki na dijital, da hakar ma’adanai da hadin gwiwar hada hadar kudi. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post