Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma jigo a jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya sake sukar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, yana zarginta da rashawa, rashin ƙwarewa, rashin fifita abubuwan da suka dace, da kuma rashin gaskiya wajen magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.
Da yake mayar da martani ga wani rahoto da ya nuna cewa rundunar sojin ƙasa ta samu kashi bakwai cikin ɗari ne kawai daga kuɗaɗen kasafin shekarar 2025 da aka ware domin kayan aikin tsaro, Atiku ya bayyana lamarin a matsayin babban abin kunya ga gwamnatin da ya ce, “batun tsaro a takarda kawai yake, ba tare da gani a fili ba”.
A cewarsa, sakin kashi bakwai cikin ɗari kawai na kuɗaɗen kayan aikin soja bai isa ba wajen fuskantar haƙiƙanin yaƙin da ake yi da matsalolin tsaro.
Dan adawar ya ce ƙarancin kuɗin da aka saki yana nuna zurfin matsalolin rashawa, rashin ƙwarewa, da rashin gaskiya a cikin gwamnati mai ci yanzu.
“Rundunar soja da ba ta da isassun kayan aiki ba za ta iya kare kanta ko ƙasar da aka ɗora mata alhakin karewa ba. Rashin isassun kuɗi yana jefa tsaron sojojinmu da ƙasar baki ɗaya cikin haɗari.
Rashin ƙwarewa da rashawa da ke haddasa jinkiri da ƙarancin sakin kuɗi su ne manyan matsalolin da ke hana magance matsalolin tsaro,” in ji Atiku.















Discussion about this post