Mutum biyu sun mutu, yayin da wasu takwas suka jikkata sakamakon rikicin da ya ɓarke tsakanin matasan ƙauyukan Inkil da Bujinji a Jihar Bauchi.
Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 11 na daren ranar 21 ga watan Yuni, 2026.
Rahotanni sun bayyana cewar, ana zargin matasan ƙauyen Inkil da kai harin ramuwar gayya kan Bujinji sakamakon wata tsohuwar taƙaddama da ke tsakanin al’ummomin biyu.
A yayin rikicin, mutum takwas sun samu raunuka.
Bayan samun kiran neman agaji, jami’an ’yansanda sun garzaya wajen tare da kai waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Ƙwararru na Jihar Bauchi domin samun kulawa.
Daga baya, likitoci sun tabbatar da mutuwar mutane biyu da aka bayyana sunayensu da Al-Amin Mohammad Aliyu da Jibir Shuaibu, dukkansu mazauna ƙauyen Inkil.
An tura jami’an tsaro zuwa yankunan da abin ya shafa domin tabbatar da zaman lafiya da kuma hana sake ɓarkewar rikicin.
Haka kuma, hukumomi sun ce suna bincike kan lamarin, kuma za a hukunta duk waɗanda aka samu da hannu a tashin hankalin.














Discussion about this post