Sojojin Operation Whirl Stroke (OPWS) tare da haɗin gwiwar jami’an Hukumar Leƙen Asiri ta Tsaro (DIA) sun kama wani mutum da ake zargi da aikata fashi da makami da kuma satar shanu a Jihar Taraba.
An kama wanda ake zargin ne da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar 21 ga watan Yuni a shingen bincike na Mbiam da ke Ƙaramar Hukumar Takum.
Rahotanni sun bayyana cewa kamen ya biyo bayan bincike da sa ido da sojoji da jami’an leƙen asiri suka yi, inda suka daɗe suna bibiyar wanda ake zargin.
An ce wanda aka kama yana cikin jerin mutanen da ake zargi da fashi da makami da satar shanu a Takum da wasu ƙauyuka.
A yanzu haka yana hannun sojoji ana ci gaba da bincike a kansa.
Hukumomin soji sun ce wannan kamen na daga cikin ƙoƙarin da ake yi na rage aikata laifuka kamar fashi da makami da satar shanu a kudancin Jihar Taraba.














