A yau Jumma’a 30 ga Janairu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya jagoranci wani taron manema labarai na yau da kullum. A lokacin taron, Guo Jiakun ya gabatar da cewa gwamnatin Sin ta nada Liu Xianfa a matsayin wakilinta na musamman kan harkokin Afirka.
Wakilin na musamman Liu Xianfa babban jami’in diflomasiyya ne kuma gogagge wanda ya saba da harkokin Afirka. Ya yi aiki a jere a matsayin babban jami’in ofishin jakadancin Sin a birnin Legas na Nijeriya, da Jakada a Kenya, da zama ma ba da taimako ga ministan harkokin waje, da kuma wakilin musamman na ofishin kwamishinan ma’aikatar harkokin waje a yankin musamman na gwamnatin Macao.
A madadin ma’aikatar harkokin waje, wakilin na musamman na kasar Sin Liu Xianfa, zai yi mu’amala da kasashen Afirka, da kungiyar tarayyar Afirka (AU), da sauran bangarorin da abin ya shafa idan akwai bukata, domin inganta tattaunawa da hadin gwiwa, da kuma yin kokari sosai wajen hada karfi da karfe don gina al’umma ta dukkan fannoni mai kyakkyawar makoma ta bai-daya a sabon zamani tsakanin Sin da Afirka. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post