An rantsar da Murtala Sule Garo a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, a wani biki da gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, ya jagoranta.
Babbar Alƙaliyar Jihar Kano, Dije Aboki, ce ta rantsar da Garo bayan karɓar rantsuwar aiki.
Manyan ‘yan siyasa da suka halarci bikin sun haɗa da tsohon gwamnan Kano kuma tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje; tsohon gwamna Ibrahim Shekarau; da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin.
Haka kuma, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Ismail Falgore, da Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II, sun halarci bikin.
Rahotanni sun nuna cewa nadin Murtala Garo ya biyo bayan murabus ɗin tsohon mataimakin gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo, bayan sauya sheƙar gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa jam’iyyar APC.















Discussion about this post