Jigo a siyasar Nijeriya, Buba Galadima, ya buƙaci tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, da ya shiga sabuwar jam’iyyar NDC domin ƙarfafa haɗin kan ‘yan adawa gabanin zaɓen 2027.
Rahotanni sun nuna cewa Galadima ya yi wannan kira ne a yayin wani taron masu ruwa da tsaki, inda ya bayyana cewa shiga jam’iyyar NDC zai taimaka wajen samar da tsari mai ƙarfi ga ‘yan adawa domin fuskantar zaɓen da ke tafe.
Ya kuma yi gargaɗin cewa rashin haɗin kai tsakanin manyan ‘yan adawa na iya janyo matsala ga nasarar su a zaɓen 2027, yana mai cewa dole ne su haɗa kai domin cimma buri ɗaya.
A cewarsa, rikice-rikicen cikin gida da ke addabar jam’iyyun adawa, musamman a NDC, na daga cikin dalilan da suka sa ake neman wata sabuwar hanyar siyasa.
Galadima ya kuma nuna cewa ana ci gaba da tattaunawa tsakanin manyan ‘yan siyasa kamar Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso kan yiwuwar komawa wata sabuwar jam’iyya domin tunkarar zaɓen 2027.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ganin akwai sauye-sauyen siyasa da yunƙurin kafa ƙawance tsakanin ‘yan adawa domin ƙalubalantar jam’iyyar APC a zaɓe mai zuwa.















Discussion about this post