ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Sake Karrama Gwamna Dauda Lawal Da Lambar Yabo Kan Mulki Na Adalci A Zamfara

by Sulaiman
2 months ago
Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya karɓi lambar yabo ta ƙwarewa daga Hukumar Daidaita Shirye-shiryen Tallafin Jinƙai ta Ƙasa (NASSCO) bisa irin ƙoƙarin gwamnatin sa wajen tabbatar da mulki na adalci da kuma aiwatar da shirye-shiryen kare marasa ƙarfi a jihar Zamfara.

An bai wa gwamnan lambar yabon ne yayin taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki da shugabannin ƙananan hukumomi da hukumar ta shirya a ɗakin taro na Transcorp Congress Hall da ke Abuja.

Hukumar NASSCO wata hukuma ce ta tarayya ƙarƙashin Ma’aikatar Harkokin Jin-ƙai da Rage Talauci, wadda ke aiwatar da shirye-shiryen tallafawa marasa galihu da ƙarfafa rayuwar masu rauni a faɗin ƙasar nan.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Dauda Lawal ya yaba wa Gwamnatin Tarayya da Bankin Duniya da sauran abokan hulɗar ci gaba bisa goyon bayan da suke bayarwa wajen ƙarfafa tsarin kariyar zamantakewa a Nijeriya.

Ya ce faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa tare da haɗa Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa (NIN) a cikin tsarin ya taimaka wajen inganta gaskiya da riƙon amana wajen rabon tallafi.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

A cewarsa, wannan taro ya zo a daidai lokacin da ake buƙatar ƙarfafa tsarin kariyar jama’a, musamman a jihohin da ke fama da matsalolin tsaro kamar Zamfara.

“Yanzu kariyar zamantakewa ta wuce batun tallafi kawai, ta zama wata muhimmiyar hanya ta tabbatar da tsaro, rage talauci da gina juriya a tsakanin al’umma,” in ji gwamnan.

Ya bayyana cewa matsalar rashin tsaro a Zamfara ta haddasa raba mutane da matsugunansu, durƙushewar hanyoyin samun abinci da kuɗaɗen shiga, lamarin da ya fi shafar mata, yara, nakasassu da mazauna karkara.

Gwamnan ya jaddada cewa dole ne shirye-shiryen tallafi su kasance masu tsari, gaskiya da amfani da sahihan bayanai domin tabbatar da cewa tallafin ya isa hannun waɗanda suka fi buƙata.

Ya kuma nuna muhimmancin ƙananan hukumomi wajen hulɗa da al’umma, tantance bayanai, tallafa wa tsarin shaidar mutum da kuma sanya ido kan yadda ake aiwatar da shirye-shiryen tallafi.

Gwamna Lawal ya ƙara da cewa, haɗa lambar NIN da Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa zai taimaka wajen rage maimaita bayanai, ƙarfafa gaskiya da kuma inganta yadda ake aiwatar da shirye-shiryen tallafi.

Sai dai ya yi gargaɗin cewa fasaha kaɗai ba za ta warware matsaloli ba idan ba tare da kyakkyawan shugabanci, riƙon amana da haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki ba.

Gwamnan ya ce, gwamnatin Zamfara na goyon bayan duk wani yunƙuri na ƙarfafa haɗin kai tsakanin gwamnatocin tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi, tare da haɗa kai da hukumomi da ƙungiyoyin ci gaba masu ruwa da tsaki a harkar kare rayuwar al’umma.

Ya kuma bayyana cewa ci gaba mai amfani ya kamata ya zarce rabon kuɗaɗe kawai, ya haɗa da bunƙasa sana’o’i, horas da matasa, noma, lafiya, ilimi, shigar jama’a cikin harkokin kuɗi da kuma ƙarfafa juriya a tsakanin al’umma.

Da take miƙa lambar yabon ga gwamnan, Babbar Mai Kula da Hukumar NASSCO ta Ƙasa, Dakta Funmi Olotu, ta ce an ba shi wannan karramawa ne saboda irin jajircewar gwamnatinsa wajen inganta kariyar zamantakewa da tabbatar da shugabanci na adalci a Zamfara.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.