ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Sake Karrama Gwamna Dauda Lawal Da Lambar Yabo Kan Mulki Na Adalci A Zamfara

by Sulaiman
4 weeks ago
Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya karɓi lambar yabo ta ƙwarewa daga Hukumar Daidaita Shirye-shiryen Tallafin Jinƙai ta Ƙasa (NASSCO) bisa irin ƙoƙarin gwamnatin sa wajen tabbatar da mulki na adalci da kuma aiwatar da shirye-shiryen kare marasa ƙarfi a jihar Zamfara.

An bai wa gwamnan lambar yabon ne yayin taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki da shugabannin ƙananan hukumomi da hukumar ta shirya a ɗakin taro na Transcorp Congress Hall da ke Abuja.

Hukumar NASSCO wata hukuma ce ta tarayya ƙarƙashin Ma’aikatar Harkokin Jin-ƙai da Rage Talauci, wadda ke aiwatar da shirye-shiryen tallafawa marasa galihu da ƙarfafa rayuwar masu rauni a faɗin ƙasar nan.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Dauda Lawal ya yaba wa Gwamnatin Tarayya da Bankin Duniya da sauran abokan hulɗar ci gaba bisa goyon bayan da suke bayarwa wajen ƙarfafa tsarin kariyar zamantakewa a Nijeriya.

Ya ce faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa tare da haɗa Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa (NIN) a cikin tsarin ya taimaka wajen inganta gaskiya da riƙon amana wajen rabon tallafi.

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

A cewarsa, wannan taro ya zo a daidai lokacin da ake buƙatar ƙarfafa tsarin kariyar jama’a, musamman a jihohin da ke fama da matsalolin tsaro kamar Zamfara.

“Yanzu kariyar zamantakewa ta wuce batun tallafi kawai, ta zama wata muhimmiyar hanya ta tabbatar da tsaro, rage talauci da gina juriya a tsakanin al’umma,” in ji gwamnan.

Ya bayyana cewa matsalar rashin tsaro a Zamfara ta haddasa raba mutane da matsugunansu, durƙushewar hanyoyin samun abinci da kuɗaɗen shiga, lamarin da ya fi shafar mata, yara, nakasassu da mazauna karkara.

Gwamnan ya jaddada cewa dole ne shirye-shiryen tallafi su kasance masu tsari, gaskiya da amfani da sahihan bayanai domin tabbatar da cewa tallafin ya isa hannun waɗanda suka fi buƙata.

Ya kuma nuna muhimmancin ƙananan hukumomi wajen hulɗa da al’umma, tantance bayanai, tallafa wa tsarin shaidar mutum da kuma sanya ido kan yadda ake aiwatar da shirye-shiryen tallafi.

Gwamna Lawal ya ƙara da cewa, haɗa lambar NIN da Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa zai taimaka wajen rage maimaita bayanai, ƙarfafa gaskiya da kuma inganta yadda ake aiwatar da shirye-shiryen tallafi.

Sai dai ya yi gargaɗin cewa fasaha kaɗai ba za ta warware matsaloli ba idan ba tare da kyakkyawan shugabanci, riƙon amana da haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki ba.

Gwamnan ya ce, gwamnatin Zamfara na goyon bayan duk wani yunƙuri na ƙarfafa haɗin kai tsakanin gwamnatocin tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi, tare da haɗa kai da hukumomi da ƙungiyoyin ci gaba masu ruwa da tsaki a harkar kare rayuwar al’umma.

Ya kuma bayyana cewa ci gaba mai amfani ya kamata ya zarce rabon kuɗaɗe kawai, ya haɗa da bunƙasa sana’o’i, horas da matasa, noma, lafiya, ilimi, shigar jama’a cikin harkokin kuɗi da kuma ƙarfafa juriya a tsakanin al’umma.

Da take miƙa lambar yabon ga gwamnan, Babbar Mai Kula da Hukumar NASSCO ta Ƙasa, Dakta Funmi Olotu, ta ce an ba shi wannan karramawa ne saboda irin jajircewar gwamnatinsa wajen inganta kariyar zamantakewa da tabbatar da shugabanci na adalci a Zamfara.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Next Post
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.