ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Sake Karrama Gwamna Dauda Lawal Da Lambar Yabo Kan Mulki Na Adalci A Zamfara

by Sulaiman
3 months ago
Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya karɓi lambar yabo ta ƙwarewa daga Hukumar Daidaita Shirye-shiryen Tallafin Jinƙai ta Ƙasa (NASSCO) bisa irin ƙoƙarin gwamnatin sa wajen tabbatar da mulki na adalci da kuma aiwatar da shirye-shiryen kare marasa ƙarfi a jihar Zamfara.

An bai wa gwamnan lambar yabon ne yayin taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki da shugabannin ƙananan hukumomi da hukumar ta shirya a ɗakin taro na Transcorp Congress Hall da ke Abuja.

Hukumar NASSCO wata hukuma ce ta tarayya ƙarƙashin Ma’aikatar Harkokin Jin-ƙai da Rage Talauci, wadda ke aiwatar da shirye-shiryen tallafawa marasa galihu da ƙarfafa rayuwar masu rauni a faɗin ƙasar nan.

ADVERTISEMENT

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Dauda Lawal ya yaba wa Gwamnatin Tarayya da Bankin Duniya da sauran abokan hulɗar ci gaba bisa goyon bayan da suke bayarwa wajen ƙarfafa tsarin kariyar zamantakewa a Nijeriya.

Ya ce faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa tare da haɗa Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa (NIN) a cikin tsarin ya taimaka wajen inganta gaskiya da riƙon amana wajen rabon tallafi.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

A cewarsa, wannan taro ya zo a daidai lokacin da ake buƙatar ƙarfafa tsarin kariyar jama’a, musamman a jihohin da ke fama da matsalolin tsaro kamar Zamfara.

“Yanzu kariyar zamantakewa ta wuce batun tallafi kawai, ta zama wata muhimmiyar hanya ta tabbatar da tsaro, rage talauci da gina juriya a tsakanin al’umma,” in ji gwamnan.

Ya bayyana cewa matsalar rashin tsaro a Zamfara ta haddasa raba mutane da matsugunansu, durƙushewar hanyoyin samun abinci da kuɗaɗen shiga, lamarin da ya fi shafar mata, yara, nakasassu da mazauna karkara.

Gwamnan ya jaddada cewa dole ne shirye-shiryen tallafi su kasance masu tsari, gaskiya da amfani da sahihan bayanai domin tabbatar da cewa tallafin ya isa hannun waɗanda suka fi buƙata.

Ya kuma nuna muhimmancin ƙananan hukumomi wajen hulɗa da al’umma, tantance bayanai, tallafa wa tsarin shaidar mutum da kuma sanya ido kan yadda ake aiwatar da shirye-shiryen tallafi.

Gwamna Lawal ya ƙara da cewa, haɗa lambar NIN da Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa zai taimaka wajen rage maimaita bayanai, ƙarfafa gaskiya da kuma inganta yadda ake aiwatar da shirye-shiryen tallafi.

Sai dai ya yi gargaɗin cewa fasaha kaɗai ba za ta warware matsaloli ba idan ba tare da kyakkyawan shugabanci, riƙon amana da haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki ba.

Gwamnan ya ce, gwamnatin Zamfara na goyon bayan duk wani yunƙuri na ƙarfafa haɗin kai tsakanin gwamnatocin tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi, tare da haɗa kai da hukumomi da ƙungiyoyin ci gaba masu ruwa da tsaki a harkar kare rayuwar al’umma.

Ya kuma bayyana cewa ci gaba mai amfani ya kamata ya zarce rabon kuɗaɗe kawai, ya haɗa da bunƙasa sana’o’i, horas da matasa, noma, lafiya, ilimi, shigar jama’a cikin harkokin kuɗi da kuma ƙarfafa juriya a tsakanin al’umma.

Da take miƙa lambar yabon ga gwamnan, Babbar Mai Kula da Hukumar NASSCO ta Ƙasa, Dakta Funmi Olotu, ta ce an ba shi wannan karramawa ne saboda irin jajircewar gwamnatinsa wajen inganta kariyar zamantakewa da tabbatar da shugabanci na adalci a Zamfara.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Auto Draft
Labarai

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Zamfara
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Zamfara
Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Next Post
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Zamfara

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Zamfara

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.