Wasu mintuna 13 a wasan Everton da Manchester City na daren ranar Litinin, inda aka sharara kwallo 6, zai iya zama babbar zagon kasa da masu masaukin bakin suka yi a gasar Premier ta bana.
City, karkashin Guardiola ce ta shige gaba da kwallo daya kafin zuwa hutun rabin lokaci, sai dai daga baya Eberton sun haye sama, inda suka zura wa City kwallo daddaya har uku.
Duk da cewa Erling Haaland ya sake cin wata kwallon, sannan kuma Jeremy Doku ya sake mayar da ta uku, aka tashi 3-3, wannan y asa City ta rasa matayinta ga Arsenal, wadda a yanzu ta yi dare-dare saman teburi.
Hakan ya sanya yanzu Arsenal ce ke da wuka da nama a kann wanda zai lashe kofin Premier na wannan shekara.
Dama an yi hasashen cewa wannan wasa zai iya zama mai wahala ga City, ganin cewa Eberton na fafutikar samun gurbin buga gasar Turai.
A karshen wasan, kocin City Pep Guardiola ya ce “gara canjaras da rashin nasara.”
”Yanzu kofin ba ya hannunmu, a baya yana hannunmu, amma yanzu ya kubuce. Muna da sauran wasanni a gaba, za mu ga yadda za ta kaya,” in ji Pep.
A yanzu Arsenal ta san cewa ita ce ke da kofi idan har ta lashe dukkanin wasanninta uku da suka rage, kuma idan ta yi nasarar hakan wannan zai zama karon farko da ta lashe kofin tun daga 2004.
Bayan yin canjaras da Eberton, yanzu mafi yawan jimillar maki da Manchester City za ta iya samu shi ne 83, inda ta lashe dukkanin wasannin gasar da suka rage mata.
Ita kuwa Arsenal a halin yanzu tana da maki 76, saboda haka idan kungiyar ta lashe dukkanin wasanninta na gasar za ta kare ne da maki 85, kuma hakan zai tabbatar musu da nasara lashe kofin Premier.
Haka nan yanzu Arsenal ce a gaba idan ana magana kan kwallye, inda take gaba da kwallo 4 a gaban City.
Amma akwai abin da zai faru a tabbatar wa Arsenal nasarar lashe gasar Premier tun daga ranar Laraba 13 ga watan Mayu.
Idan Arsenal ta yin nasara a kan West Ham a ranar Lahadi, ita kuma Manchester City ta yi rashin nasara a karawarta da Brentford a ranar Asabar, sannan City ta sake yin rashin nasara a hannun Crystal Palace a wasanta na gaba, Arsenal za ta lashe kofin Premier kafin wasanta biyu na karshe.
To amma idan dukkanin kungiyoyin biyu suka ci gaba da samun nasara a wasanninsu, ba za a san wanda zai lashe kofin ba har sai a ranar karshe ta gasar.
“Hakin da ake ciki Manchester City na cikin tsaka mai wuya, amma dole ne su natsu, su fuskanci abin da ke gabansu,” in ji tsohon dan wasan Blackpool Charlie Adam a tattaunawarsa da gidan rediyon BBC 5 Libe.
Amma kuma har yanzu akwai abubuwan mamaki da za su iya faruwa.















Discussion about this post