ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

by Sulaiman and Abba Ibrahim Wada
4 weeks ago
Premier

Wasu mintuna 13 a wasan Everton da Manchester City na daren ranar Litinin, inda aka sharara kwallo 6, zai iya zama babbar zagon kasa da masu masaukin bakin suka yi a gasar Premier ta bana.

City, karkashin Guardiola ce ta shige gaba da kwallo daya kafin zuwa hutun rabin lokaci, sai dai daga baya Eberton sun haye sama, inda suka zura wa City kwallo daddaya har uku.

Duk da cewa Erling Haaland ya sake cin wata kwallon, sannan kuma Jeremy Doku ya sake mayar da ta uku, aka tashi 3-3, wannan y asa City ta rasa matayinta ga Arsenal, wadda a yanzu ta yi dare-dare saman teburi.

ADVERTISEMENT

Hakan ya sanya yanzu Arsenal ce ke da wuka da nama a kann wanda zai lashe kofin Premier na wannan shekara.

Dama an yi hasashen cewa wannan wasa zai iya zama mai wahala ga City, ganin cewa Eberton na fafutikar samun gurbin buga gasar Turai.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

A karshen wasan, kocin City Pep Guardiola ya ce “gara canjaras da rashin nasara.”

”Yanzu kofin ba ya hannunmu, a baya yana hannunmu, amma yanzu ya kubuce. Muna da sauran wasanni a gaba, za mu ga yadda za ta kaya,” in ji Pep.

A yanzu Arsenal ta san cewa ita ce ke da kofi idan har ta lashe dukkanin wasanninta uku da suka rage, kuma idan ta yi nasarar hakan wannan zai zama karon farko da ta lashe kofin tun daga 2004.

Bayan yin canjaras da Eberton, yanzu mafi yawan jimillar maki da Manchester City za ta iya samu shi ne 83, inda ta lashe dukkanin wasannin gasar da suka rage mata.

Ita kuwa Arsenal a halin yanzu tana da maki 76, saboda haka idan kungiyar ta lashe dukkanin wasanninta na gasar za ta kare ne da maki 85, kuma hakan zai tabbatar musu da nasara lashe kofin Premier.

Haka nan yanzu Arsenal ce a gaba idan ana magana kan kwallye, inda take gaba da kwallo 4 a gaban City.

Amma akwai abin da zai faru a tabbatar wa Arsenal nasarar lashe gasar Premier tun daga ranar Laraba 13 ga watan Mayu.

Idan Arsenal ta yin nasara a kan West Ham a ranar Lahadi, ita kuma Manchester City ta yi rashin nasara a karawarta da Brentford a ranar Asabar, sannan City ta sake yin rashin nasara a hannun Crystal Palace a wasanta na gaba, Arsenal za ta lashe kofin Premier kafin wasanta biyu na karshe.

To amma idan dukkanin kungiyoyin biyu suka ci gaba da samun nasara a wasanninsu, ba za a san wanda zai lashe kofin ba har sai a ranar karshe ta gasar.

“Hakin da ake ciki Manchester City na cikin tsaka mai wuya, amma dole ne su natsu, su fuskanci abin da ke gabansu,” in ji tsohon dan wasan Blackpool Charlie Adam a tattaunawarsa da gidan rediyon BBC 5 Libe.

Amma kuma har yanzu akwai abubuwan mamaki da za su iya faruwa.

Premier
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
Premier
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
An Kama Bello Bodejo Bayan Ya Yi Wa Magoya Bayansa Jawabi A Taraba

An Kama Bello Bodejo Bayan Ya Yi Wa Magoya Bayansa Jawabi A Taraba

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.