ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

by Sulaiman and Abba Ibrahim Wada
2 months ago
Premier

Wasu mintuna 13 a wasan Everton da Manchester City na daren ranar Litinin, inda aka sharara kwallo 6, zai iya zama babbar zagon kasa da masu masaukin bakin suka yi a gasar Premier ta bana.

City, karkashin Guardiola ce ta shige gaba da kwallo daya kafin zuwa hutun rabin lokaci, sai dai daga baya Eberton sun haye sama, inda suka zura wa City kwallo daddaya har uku.

Duk da cewa Erling Haaland ya sake cin wata kwallon, sannan kuma Jeremy Doku ya sake mayar da ta uku, aka tashi 3-3, wannan y asa City ta rasa matayinta ga Arsenal, wadda a yanzu ta yi dare-dare saman teburi.

ADVERTISEMENT

Hakan ya sanya yanzu Arsenal ce ke da wuka da nama a kann wanda zai lashe kofin Premier na wannan shekara.

Dama an yi hasashen cewa wannan wasa zai iya zama mai wahala ga City, ganin cewa Eberton na fafutikar samun gurbin buga gasar Turai.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

A karshen wasan, kocin City Pep Guardiola ya ce “gara canjaras da rashin nasara.”

”Yanzu kofin ba ya hannunmu, a baya yana hannunmu, amma yanzu ya kubuce. Muna da sauran wasanni a gaba, za mu ga yadda za ta kaya,” in ji Pep.

A yanzu Arsenal ta san cewa ita ce ke da kofi idan har ta lashe dukkanin wasanninta uku da suka rage, kuma idan ta yi nasarar hakan wannan zai zama karon farko da ta lashe kofin tun daga 2004.

Bayan yin canjaras da Eberton, yanzu mafi yawan jimillar maki da Manchester City za ta iya samu shi ne 83, inda ta lashe dukkanin wasannin gasar da suka rage mata.

Ita kuwa Arsenal a halin yanzu tana da maki 76, saboda haka idan kungiyar ta lashe dukkanin wasanninta na gasar za ta kare ne da maki 85, kuma hakan zai tabbatar musu da nasara lashe kofin Premier.

Haka nan yanzu Arsenal ce a gaba idan ana magana kan kwallye, inda take gaba da kwallo 4 a gaban City.

Amma akwai abin da zai faru a tabbatar wa Arsenal nasarar lashe gasar Premier tun daga ranar Laraba 13 ga watan Mayu.

Idan Arsenal ta yin nasara a kan West Ham a ranar Lahadi, ita kuma Manchester City ta yi rashin nasara a karawarta da Brentford a ranar Asabar, sannan City ta sake yin rashin nasara a hannun Crystal Palace a wasanta na gaba, Arsenal za ta lashe kofin Premier kafin wasanta biyu na karshe.

To amma idan dukkanin kungiyoyin biyu suka ci gaba da samun nasara a wasanninsu, ba za a san wanda zai lashe kofin ba har sai a ranar karshe ta gasar.

“Hakin da ake ciki Manchester City na cikin tsaka mai wuya, amma dole ne su natsu, su fuskanci abin da ke gabansu,” in ji tsohon dan wasan Blackpool Charlie Adam a tattaunawarsa da gidan rediyon BBC 5 Libe.

Amma kuma har yanzu akwai abubuwan mamaki da za su iya faruwa.

Premier
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Premier
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
An Kama Bello Bodejo Bayan Ya Yi Wa Magoya Bayansa Jawabi A Taraba

An Kama Bello Bodejo Bayan Ya Yi Wa Magoya Bayansa Jawabi A Taraba

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.