Babban aikin jigilar ruwa na “Lesotho Highlands Water Project”, ko kuma LHWP a takaice, ya samu sabon sakamako a matakinsa na biyu dake karkashin ginawa, inda a ranar Laraba da ta gabata, aka kaddamar da sabuwar gada ta Senqu, wadda ta kasance wani bangare na aikin.
Wasu kamfanonin kasar Sin ne ke daukar nauyin gudanar da aikin gina LHWP, inda suka samar da guraben aikin yi fiye da dubu 17 ga mutanen wurin, da ba su horo a fannin fasahohin aiki, ta yadda aka mai da aikin LHWP din wani misali na hadin gwiwar Sin da Afirka mai amfanin juna.
Manyan kusoshin da suka halarci bikin kaddamar da gadar Senqu sun hada da sarkin Lesotho, Letsie na uku, da shugaban kasar Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa.
Cikin jawabin da ya bayar wajen bikin kaddamarwar, sarki Letsie na uku na kasar Lesotho ya ce, sabuwar gadar ta wuce matsayin wata nasara a fannin raya kayayyakin more rayuwa, wadda za ta ba da damar hadewar mabambantan al’ummu, da karfafa hadin gwiwa, da haifar da ci gaban tattalin arziki a dukkan kasashen Lesotho da Afirka ta Kudu.
Kana a nasa bangare, shugaba Cyril Ramaphosa na kasar Afirka ta Kudu ya ce, aikin karkata ruwa na LHWP aiki ne da kasarsa ta zuba mafi yawan kudi, cikin dukkan ayyukan da ta samar da kudi wadanda suka kasance a kasashen waje.
Kana ruwan da za a samar ta wannan aiki zai biya bukatar kasar Afirka ta Kudu a fannin raya kasa, ta la’akari da yanayin karancin ruwa da kasar ke fama da shi yanzu. (Bello Wang)















Discussion about this post