An shiga cikin firgici a garin Jalingo da ke a cikin jihar Taraba bayan an ji hare-haren bindiga kusa da shalkwatar hukumar zabe mai zaman kanta INEC da ke Jalingo.
Ba san abinda ya janyo harbin ba amma wata majiya ta ce, an samu rashin jituwa ne a tsakanin wasu jami’an tsaro da wakilan wasu jam’iyyu.
- Da Dumi-Dumi: Kakakin Majalisar Dokokin Zamfara Da Mataimakinsa Sun Sha Kaye
- INEC Ta Lashi Takobin Yin Nazari Kan Daukacin Almundahar Zabe
Hakan ya janyo masu shaguna sun kulle shagunan su mutane kuma sun kwarace wa titunan garin inda kuma iyaye suka garzaya makarantu don kwaso ‘ya’yan su.
Kakakin rundunar ‘yansanda na jihar ASP Usman Abdullahi, bai fitar da wata sanarwar kan lamarin ba har lokacin da aka hada wannan rahoton.