Manoman Tumatir kimanin su 100 aka horar, kan sarrafawa da sayar da shi, tare kuma da rage yawan asarar da suke yi bayan noma shi.
Kazalika, an horar da su a kan yadda za su rika ba shi kariya daga dumamar yanayi.
Horon, wanda ya gudana a garin Zariya da ke Jihar Kaduna, shirin cibiyar gudanar da bincike ta Afirka (FAR-LeaF II), ta yi horon ta hanyar hadaka da cibiyar NSPRI ta kasa, da kuma cibiyar NIFAAS da sauran abokan hadaka.
Shugabar taron a yawabinta a wajen horon, Dakta Ololade-Latifat Abdulrahman ta sanar da cewa; an kirkiro shirin ne, domin dakile barazanar dumamar yanayi da ke yi wa nomansa illa, tare da inganta rayuwar dubban ‘yan Nigeriya da suka dogara a kan amfanin gona.
Har ila yau, ta danganta Tumatari a matsayin wani abu mai matukar muhimmanci a abinci da samar da kudaden shiga ga masu nomansa da kuma samar da ayyukan yi, ga miliyoyin ‘yan kasa.
Haka zalika, Dakta Ololade, ta sanar da cewa; karancin ruwan sama da sauyin yanayi da cututtukan da ke lalata shi da kuma yawan asarar da manomansa ke fuskanta, na jawo koma baya ga nomansa.
A cewar tata, wannan horo na da matukar muhimmanci, domin kuwa zai kara taimaka wa wadanda suka amfana da shi wajen kara yawan girbi mai yawan gaske da rage asara da samar da ayyukan yi da kuma samar da wadatarsa a daukacin fadin kasar.
Ta kara da cewa, horon na daga cikin aikin yakar dumanar yanayi na Tumatir wato, CBACTBCA, wanda ya yi duba a kan illar dumamar yanayi ga masu ruwa da tsaki a fannin na nomansa, tare da kara karfafa guiwar rungumar dabarun nomansa.
Ta ci gaba da cewa, bincike ya nuna cewa; akwai bukatar kara habaka samar da daukin da zai taimaka wa manomansa, masu sarrafa shi da sayar da shi da kuma yin safararsa, musamman domin su rungumi tsarin kaucewa dumamar yanayi da ke yi masa illa.
Bugu da kari, Dakta Ololade ta bayyana cewa; wadanda suka amfana da horon, za a raba musu ingantaccen Irin Tumatir da sauran kayan zamani na rage dumamar yanayi.
Ta kuma yaba wa shirin na FAR-LeaF II da Cibiyar NSPRI da NIFAAS da kuma sauran abokan hadaka, kan gudunmawar da suka bayar ga shirin.
Shi ma a nasa jawabin a wajen horon, wani manomi da ya amfana da horon, kuma Malamin Aikin Gona daga Hukumar Bunkasa Aikin Gona ta Jihar Kaduna (KADA), Malam Aliyu Umar, ya sanar da cewa; ya amfana da horon, musamman kan yadda manoman Tumatirin, za su rage yin asara bayan sun yi girbi.
Ya ce, ingantaccen Irin na Tumatir da aka raba wa mahalarta horon, zai taimaka wa manoman, musamman wajen rage dumamar yanayi, yayin da suka shuka shi.
Wata manomiyar Tumatir, wadda ita ma ta amfana da horon, Malama Asibi Hassan, wacce ta fito daga Karamar Hukumar Sabon Gari da ke Jihar Kaduna ta sanar da cewa; horon ya zo a kan gaba, musamman duba da yadda mahalartansa suka samu ilimi kan yadda za su adana Tumatirin da suka girbe.
Ta kuma danganta tashin farashinsa a wasu sassan kasar, sakamakon karancin kayan aiki na zamani da na adana shi, inda ta sanar da cewa; akasarin Tumatirin da aka noma, na lalacewa a hanya ne kafin ya isa kasuwa.
Malama Asibi, ta kuma yi kira ga matakan gwamnati uku na kasar da sauran abokan hadaka a fannin na nomansa, da su taimaka wajen bai wa manomansa horo da samar musu da kayan aiki na zamani da sauran makamantansu.














