A yau Talata ne aka wallafa makalar shugaban kasar Sin Xi Jinping a wasu kafofin watsa labaran kasar Masar kafin isar shugaban birnin Alkahira, fadar mulkin kasar ta Masar domin ziyarar aiki. Babban taken malakar da aka wallafa a jaridar Al-Ahram, da jaridar Al Akhbar, da kuma jaridar Al Gomhuria, shi ne “Hadin gwiwa na tsawon shekaru 70, bude sabon babi bisa himma da kwazo”.
A cewar shugaba Xi, Sin da Masar sun kulla huldar diflomasiyya a hukumance shekaru 70 da suka gataba. Kuma bisa hadin gwiwarsu cikin shekaru 70 da suka gabata, dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta kasance abin koyi, a fannin habaka hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Larabawa da ma kasashen Afirka, kana abin koyi game da yadda ake sada zumunci, da karfafa hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa.
Ya ce a nan gaba kuma, kasar Sin na fatan yin hadin gwiwa da Masar domin inganta ci gaban kasashen, tare da karfafa dangantaka tsakanin kasashen biyu.Ban da haka kuma, tun daga yau Talata 1 ga watan Satumba, an fara nuna wani shirin bidiyo da kafar yada labarai ta CMG ta kasar Sin ta tsara, mai taken “Tsoffin bayanai da Xi Jinping yake so” a harshen Larabci ta wasu manyan kafofin watsa labaran kasar Masar.
A sa’i daya kuma, an fara watsa shirin bidiyo mai taken “Abin da na karu bayan karanta littafin ‘Me Xi Jinping ya ce game da gudanar da harkokin kasa da na siyasa’” ta kafar talabijin na harshen Rashanci na kafar CGTN, da Gidan rediyo da talabijin na kasar Kyrgyzstan, bisa hadin gwiwar CMG da Gidan rediyo da talabijin na kasar Kyrgyzstan, da kuma Babbar jami’ar kasar Kyrgyzstan. (Mai Fassara: Maryam Yang)














