An kaddamar da babban taron yayata manufofi dangane da bikin baje kolin kasa da kasa na kasar Sin, na hajojin da ake shigowa da su daga sassan ketare ko CIIE, da taron kasa da kasa na dandalin tattauna batutuwan tattalin arziki na Hongqiao ko HQF karo na tara, a jiya Laraba a hedkwatar kungiyar tarayyar Afirka ta AU dake birnin Addis Ababa, fadar mulkin kasar Habasha.
Mahalarta tarukan biyu sun karfafa bukatar amfani da damammaki na musamman, kuma masu karfi da tarukan ke samarwa wajen bude karin kafofin shiga katafariyar kasuwar kasar Sin, da gaggauta bunkasa masana’antun kasashen Afirka.
Da yake jawabi yayin taron, daraktan sashen masana’antu, ma’adanai, sana’o’i da yawon bude ido a hukumar gudanarwar AU mista Ron Osman Omar, ya yi karin haske game da daga matsayin dangantakar Sin da Afirka zuwa hadin gwiwa daga dukkanin fannoni, wanda baya ga amincin siyasa, hakan ya kuma shaida bunkasar hadin gwiwa a fannonin raya tattalin arziki da neman ci gaba, yana kuma taka rawar gani wajen ingiza muradun kasashe masu tasowa.
Omar, ya kara da cewa dangantakar dake tsakanin kasashen Afirka da Sin ta kai wani matsayi mai cike da karsashi da zurfi. Kazalika, baje kolin CIIE ya gabatarwa ‘yan kasuwar Afirka da muhimmin dandali, mai samar da kafa ta kara fadada yawan hajojin da ake fitarwa zuwa sassan ketare, da hade su cikin tsarin daga darajar hajoji da ake hada-hadarsu.
A nasa jawabin kuwa, shugaban tawagar kasar Sin a kungiyar AU Jiang Feng, cewa ya yi baje kolin CIIE na Sin shi ne irinsa na farko a duniya da aka tsara musamman domin ingiza shigo da hajoji, wanda kuma ke zama muhimmin dandali na ingiza babban matsayin bude kofar kasar Sin, da raba damammakin neman ci gaba tare da sauran sassan duniya.
Jiang Feng, ya kara da cewa a shekarun baya-bayan nan, sannu a hankali kasar Sin na ci gaba da fadada kawar da dukkanin harajin fito kan hajojin kasashen Afirka da ake shigarwa cikin kasar, da saukaka hidimomin kwastam, da kyautata yanayin gudanar da cinikayya, ta yadda hakan zai bayar da damar kawar da shingaye, da fadada kafofin shigar da karin hajojin kasashen Afirka cikin babbar kasuwar kasar Sin. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post