Majalisar Dattawa ta tabbatar da Muttaqha Rabe Darma a matsayin minista bayan kammala tantance shi a majalisar, amincewar ta biyo bayan zaman tambayoyi da amsoshi da aka yi da shi kafin yanke hukunci.
Kafin hakan, Shugaban Kasa Bola Tinubu ya aike wa majalisar wasiƙa a ranar Laraba, inda ya nemi a tantance tare da amincewa da Darma a matsayin minista. Wannan mataki ya zo ne bisa tanadin doka da ke bai wa majalisar ikon tantance nade-naden gwamnati.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya karanta wasiƙar shugaban kasa sannan ya mika batun ga Kwamitin Majalisun tarayya biyu domin ci gaba da aiki a kai tare da ba su umarnin su gabatar da rahoto cikin gaggawa.
Daga bisani, majalisar ta amince da nadin Darma bayan kammala dukkan matakan da suka dace, yayin da ake sa ran ƙarin bayani kan nadin zai fito nan gaba.















Discussion about this post