An yi taron kara wa juna sani na kasa da kasa kan tunanin Xi Jinping a fannin al’adu karo na biyu jiya Lahadi 6 ga watan nan a birnin Shenzhen na lardin Guangdong da ke kudancin kasar Sin. Taron mai taken “inganta jigon al’adu don zamanantar da kasar Sin”, ya samu halartar wasu kwararru da masana gami da wakilai kimanin 130, daga cibiyoyin nazari da jami’o’in kasar Sin gami da cibiyoyin nazarin tunanin Xi Jinping a fannin al’adu da wayar da kan al’ummar kasar Sin na kasasehn waje.
Mataimakin shugaban sashen yayyata ayyukan kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, Hong Dayong, ya gabatar da jawabi a gun bikin kaddamar da taron, inda ya ce, inganta ginshikin al’adu na bukatar zurfafa karatu gami da kara fahimtar tunanin shugaba Xi Jinping a fannin al’adu, da tsayawa ga ayyukan yin kirkire-kirkiren al’adu, gami da karfafa mu’amala da koyi da juna a fannin wayar da kan al’umma, yayin da ake ci gaba da nazari da kuma gadon tarihi da al’adun al’ummar kasar Sin. (Murtala Zhang)














