Ana ci gaba da yin dukkan kokari domin ceto mutane 2 da har yanzu ba a gani ba, biyo bayan mummunan hatsarin da ya auku a wani wurin hakar kwal, a lardin Shanxi na arewacin kasar Sin.Yayin wani taron manema labarai da aka yi jiya Asabar da dare, magajin garin Changzhi Chen Xiangyang, ya ce an samu fashewar gas a wurin hakar kwal na Liushenyu dake gundumar Qinyuan ta garin Changzhi, da misalin karfe 7:29 na yammacin ranar Juma’a, inda aka tabbatar da jimilar mutane 82 sun mutu, yayin da 2 suka bata.
A cewarsa, jimilar mutane 128 ne suka jikkata kuma suke karbar kulawa a asbiti. Jami’ai sun bayyana yayin taron manema labaran cewa, hargitsi a wurin da hatsarin ya auku da kuma gazawar kamfanin na bayar da sahihin adadin ma’aikatan da ke bakin aiki a lokacin aukuwar lamarin ne suka yi sanadiyyar bayar da alkaluma na kuskure da aka gabatar da farko.
Magajin garin ya kuma bayyana cewa, bayan binciken da aka yi na farko, an samu kamfani mai kula da hakar kwal din da mummunan laifin keta dokoki. Kuma tuni aka dauki mataki kan wadanda ke da alhaki, kana an dakatar da ayyukan hakar kwal, domin yi wa matakan tabbatar da tsaro da amincin aiki garambawul.
Gwamnatin lardin ta tura jami’ai 775 zuwa wurin, cikin su har da ma’aikatan ceto da jami’an kiwon lafiya. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post